Saturday, December 11, 2010

YADDA AKA TARBI DAWOWAR SU MALAM YAKUBU YAHAYA KATSINA photo: abdul'aziz

MALAM YAKUBU YANA YIWA 'YAN UWA JAWABI AKAN ZUWAN SU IRAN

NAN KUMA TARON MUTANAN DA SUKA ZO YIWA MALAM BARKA DA ZUWA

NAN MA 'YAN UWA NE TARE DA MAKWABTAN MALAM

WASU DAGA CIKIN 'YAN UWA

MALAM YANA YANA FADIN ABUBUWAN DA 'YAN UWA YA KAMATA SU RIKAYI..

Tuesday, December 7, 2010

DA'IRAR KATSINA TA FARA GABATAR DA ZAMAN MAKOKIN IMAM HUSAINI AMINCIN ALLAH YA TABBATA A GARE SHI


Daga: AbdulAzizi
A yau Talata ne 2 ga watan al-Muharram 1432, Da'irar 'yanuwa Musulmi almajiran Malam Zakzaky Allah Ya kiyaye shi  ta Katsina da kewaye ta fara gabatar da karatun juyayin Ashurar Imam Husaini aminci ya tabbata a gare shi.

A gabatarwar da ya yi, Malam Sabo ATC, ya bayyana cewa, Ita waki'ar Ashura ba al'amari bane wanda ya kebanci 'Yan Shi'a ba kadai, a a al'amari ne na Musulunci kacokaf. Ya karanto wasu daga cikin Hadisan da aka ruwaito daga  cikin litattafan  ahluss Sunnati, ruwayoyin da aka karbo su daga Manyan Sahabban Manzon Allah.

Ya karanto ruwayoyin da suka yi bayanin kisan da za a yi wa Imam Husaini din tun Annabi tsira da amincin Allah su tabbata gare shi yana raye, inda suka nuna Manzon Allah ya yi kuka, kuma Sahabbansa sun taya shi wannan kuka na kisan da makiyansa daga cikin wannan al'umma tasa zasu yi akan wannan jika nasa mai daraja.

Ga wasu daga cikin hotunan wannan zama na makoki nan da aka dauka a wannan rana ta farko.
Harisawa suna sauraen karatu a zaman makokin da aka fara gabatarwa a Katsina
'Yanuwa maza suna sauraren karatun daga Malam Sabo ATC a ranar farko ta ta'aziyyar  kisan Imam Husaini
Wani sashe na 'yanuwa mata a lokacin gabatar da karatun Ashura a Katsina

'Yanuwa na sashen kiwon lafiya a wajen karatun Ashurar Imam Husaini a Katsina

Sunday, December 5, 2010

BIKIN YAYE DALIBAI MATA NA FUDIYYAH KATSINA TARE DA SAUKAR KARATUN AL'QUR'ANI MAI GIRMA NA DALIBAN DA KE KARATU A MAKARANTUN SAKANDARE

Daga: AbdulAzizi


An bayyana aibin Ilmi da cewa shine rashin aiki da shi.Malam Bashir Kankia ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen bikin yaye dalibai mata na makartantar Fudiyyah katsina,da suka kammala karatunsu a matakin farko da aka gabatar a markazin ‘yanuwa dake katsina, a ranar Lahadi 29/ 12/ 1431.
Malam bashir Kankia, ya fadakar da ‘yanuwa gabadaya  wajabcin dake da akwai na aiki da Ilimin da Allah (T) ya sanar da mutum, ya kuma tsoratar da ‘yanuwan akan rashin aiki da Ilimi, inda ya karanto kissar bil’am dan Ba’ura da Allah ya bayar a cikin Qur’ani mai tsarki, da kuma mummunan karshen da  ya yi sakamakon take sanin da ya yi. Malam bashir  ya ce,Ilimi yana da dadi kuma yana da hadari,kuma hadarinsa shine rashin aiki da shi. Sannan  ya ce, “idan baka aikata abinda ka koya ba,to tabbas zaka manta da wannan abin da ka koya”, sannan yace, duk wanda ya yi aiki da abinda ya sani ,to Allah zaya gada masa ilimin abinda bai sani ba . sannan ya tabbatar da cewa,idan muka yi  aiki da Ilmi, zaya haifar mana dab alkhairi Duniya da Lahira.Sai ya nemi ‘yanuwa da su roki Allah ya  basu Ilimi da lafiya, lafiyar kuma itace aiki da Ilimin.
A karshe Malam bashir ya  yi kira ga ‘yanuwa mazansu da matansu da su nuna ma ‘ya’yansu karatu da aiki da shi, ya ce, idan ba haka ba , suma yaran ba zasu yi aiki da karatu ba. Ya ce,’Annabawa da Imamai da sauran bayin Allah na kwarai, basu tara dukiya ba, domin su abin koyi ne, da dukiya suka tara da sun bar abin koyi. Sai ya karfafa da cewa, Maulanmu Malam Zakzaky(H) shi ma ba dukiya yake koyarda Tarawa ba, amma dai yana koyar da mu Ilimi ne,Sai ya yi kira ga dukkan ‘yanuwa da su riki Malam Abin koyinsu”mu ji tsoron Allah sai ya sanar damu”.
A tun farko da yake jawabin maraba, shugaban makarantar Malam Kabir Sani, ya dan gutsuro tarihin makarantar  bangaren ‘yanuwa matan ,inda ya bayyana cewa, su dai ‘yanuwa matan sun fara wannan karatu  tsawon shekaru,amma rashin jurewa ga halartar makarantar ya sa sai a wannan karo aka fara yaye su  a matsayin karatu mai tsayayyen lokaci na shekara biyar a matakin farko. Sai ya yi kira ga iyaye da mazajen matan da su bayar da cikakken hadin kai domin cimma abin da aka sa a gaba.
Shi dai wannan biki na yaye dalibai bangarori uku ne aka shirya ma shi, bangaren karatun shekara biyar, sai  kuma wani bangaren na sheka uku da Malam Yakubu Yahaya ya kaddamar domin bada horo ga ‘yanuwa mata da zasu iya koyarwa koda a mataki na kananan makarantu, gami da wa’azantarwa. Sanan sai bangaren yaran da suke a makarantun boko inda ake basu karatun addini su kuma sun sami kamala kartun al’qur’ani ne.
A karshen taro an bayar da takardun shedar kamala karatu a wadancan matakai guda biyu sannan  daliban da suka yi saukar al’qur’ani  suka karanto wasu sassa na surorin al’qur'anin, inda daga karshe aka bayar da kyututtuka ga bangarori daban-daban da suke bayar da gudunmuwarsu a ci gaban wannan karatu.

Bangaren daliban da suka sauke al'qur'ani mai girma a yayin bikin da aka shirya masu a Katsina
Daliban da suka kammala karatunsu na tsawon shekaru biyar a yayin da ake gabatar da walimar kammala karatun da aka shirya masu


 Sashen yanuwanda suka kammala karatun su na shekaru uku a makarantar fudiyyah katsina a bikin da aka gabatar domin taya su murna

 
Wani bangare na 'yanuwa mata suna sauraren jawabin da aka gabatar a wajen walimar kammala karatunsu  a Fudiyyah Katsina

ZIYARAR DANDALIN MATASA A ASIBITIN MASU FAMA DA RASHIN HANKALI

 Daga:Abdul Azizi
Bangaren Dandalin Matasa na harkar Musulunci da Malam Zakzaky(H) yake yi ma jagoranci da  ke  Katsina ya kai ziyarar bada agaji a asibitin masu fama da rashin lafiyar tabin hankali dake cikin birnin Katsina, a ranar Litinin 23/ 12/ 1431 albarkacin bukukuwan Idil gadeer.  

Shamsuddini Ahmad yana mika kyauta ga daya daga cikin masu kula da marasa lafiyar
 
 
Da yake gabatar da takaitaccen bayani bayan kammala wannan ziyara, Malam AbdulKarim Usamatu ,ya bayyana cewa, matashi shine fata da al'umma ke da ita, kuma wannan harka ta addini da Malam(H) ke yi ma jagoranci tana alfahari da matasa.Sai ya ce, wannan harka da Malam (H)yake yi ma jagoranci mune ake so mu yi dakon ta zuwa ga al'umma. Ya ce, idan matashi bai yi addini ba, to dole ne kuma ya yi wani abu daban wanda kuma ba addinin ba ne.sai ya shawarci matasan dasu tsayu akan al'amarin addini domin su bar kyakkyawan ambato ga masu zuwa nan gaba tare da samun kyakkyawan sakamako gobe kiyama. ya ja hankalin matasa dasu  gode ma Allah(T) da ya yi masu baiwa da fahimtar addini a irin wannan lokaci.
Ita dai wannan  ziyara 'yanuwan na dandalin matasa sun gabatar da ita ne karkashin jagorancin Shamsuddini Ahmad, 'yanuwa maza da mata ne suka rufa masa baya yayin gabatar da wannan ziyarar, inda kuma suka sami tarba daga Jami'an da ke kula da marasa lafiyar tare da nuna farincikinsu da kawo wannan ziyara.
Andai zagaya da su matasan inda suka ga yanayin marasa lafiyar gami da bayar da kyutuka garesu albarkacin wanna rana ta gadeer mai girma.
Yanuwa na dandalin matasa yayin da suka kai ziyara a asibitin masu fama da lalurar rashin hankali

Yanuwa na dandalin matasa tare da Jami'an asibitin a lokacin da suka kai ziyarar
Yanuwa mata na dandalin matasa a yayin ziyarar da suka kai a Asibiti marasa hankali da ke Katsina

Friday, November 26, 2010

YADDA DA'IRAR KATSINA TA GABATAR DA IDIL GADEER A SHEKARAR 1431

Daga: Abdulazizi / Zaharadden
                                                                        
                
A ranar Juma'a 20 ga watan Zul-Hijja  1431 Hijiriyyah, wanda ya zo daidai da 26 / 11/ 2010 Miladiyyah, Da'irar 'yanuwa Musulmi almajiran Sayyeed Ibrahim Zakzaky(H) ta katsina ta gabatar da taron wa'azin murnar Idil Gadeer na wannan Shekara ta 1431, a harabar masallacin Juma'a dake cikin birnin Katsina.
Taron wanda ya fara da misalin karfe hudu da rabi na yammacin ranar ta Juma'a, an bude shi ne da karanto wasu daga cikin ayoyin al-Qur'ani mai tsarki da ga bakin dan uwa Malam Adamu Gobarau. Bayan sa ne sai Malam Sabo ATC ya gabatar da 'yan wasan kwaikwayo na Dan Fodiyo, inda Malam Ahmad Kofar Sauri ya jagoranci gabatar da 'yanwasan, inda suka gabatar da wata Tamsiliyya mai kayatarwa mai suna "CIN AMANA". tamsiliyyar ta yi nuni ne da abubuwan da suka faru a tarihi na canja wakilcin da Manzon Allah (SAWW) ya yi, tare da kawo wasu abubuwa da suka shafi hana Sayyida  Zahara(AS) gadonta gami da zuwa gidanta da aka yi aka banka kyauren da ya yi sanadiyyar zubewar cikin da take dauke da shi Na Muhsin da kuma yin sanadiyyar Shahadarta daga bisani. Masu gabatar da tammsiliyyar sun yi kokarin isar da sakon nasu cikin hikima tare da sakaya sunayen duk masu hannu a afkar da wannan waki'a.

Daga nan ne sai aka ba mawakan gwagwarmaya dama suma suka bada tasu gudunmuwa ta hanyar wake Imam Ali Zakin Allah.(AS).
Wanda ya gabatar da jawabi a wannan taro shi ne Malam Shehu Usman Dalhatu  Karkarku a madadin Malam Yakubu Yahaya. Mal Shehu ya bayyana cewa Wannan Munasaba ta Gadeer ,Munasaba ce da ta shafi dukkan Musulmi ba 'yan shi'a ba. Munasaba ce wadda Manzon Allah ya kama hanun ImamAli(AS) ya daga sama, sannan ya ce "wanda na kasance Shugabansa, to ga Ali nan shine Shugabansa" san ya yi Addu'a da cewa"Allah ka taimaki wanda ya taimake shi, ka kuma watsar da wanda ya watsar da shi" . Sanna sai ya jawo hankalin Musulmi da cewa, wannan al'amari ba siyasa bace kamar yadda wasu suke gani, a'a addini ne. Malamin ya ce ,ko da yake bayan Manzon ya yi wafati,wasu sun sun canja sun zabi na su shugaba. Saannan sai ya yi tambaya ga masu ganin 'yan shi'a basu yarda da wannan canji ba da wasu suka yi akan na Manzo da cewa, wasu Sahabban suma  basu yi bai'a ba ga wannan canji, su ya ya zaka ce masu?
da ya juya kan yadda aka kirkiro Hadisai na karya, irin masu nuna cewa' wai Manzo ya ce" abi shugaba, na kirki ne ko  fajiri" sai ya ce irin wadannan Hadisai ne suka sa musulmi suke bin Fajiran shugabanni abinda ya kai su ga bin jagorancin kafirin Shugaba. Sannan yace " idan ka damfara jagorancinka ga wanda ba Manzo ne ya ayyana shi ba, to bai yi daidai ba"

Sannan ya jawo hankalin al'umma da cewa Manzo ya yi umurnin Duk wanda ya ji wannan sako , ya isar da shi ga  wanda bai ji ba, Uba ya isar ma da 'ya'yansa, 
A karshe ya bayyana cewa, idan har addini ba shi da jagoranci iriin wanda Manzo ya kafa, to dole ne za a ci gaba da zama cikin rigingimu, kuima idan ka rasa jagorancin Imam Ali (AS) zaka ci gaba da zama karklashin jagorancin Fajirai.
 Ya yi fatan Allah (T) ya amsa mana wannan Wila'a da  muka yi ga Imam Ali (AS) a karkashin jagorancin Sayyeed Zakzaky(H).


Wani bangare na 'yanuwa suna sauraren jawabin da Malam Shehu Karkarku ya gabatar a wajen taron Gadeer da Da'irar Katsina ta gabatarta


'Yanuwa mata suna sauraren jawabin Gadeer da aka gabatar a Katsina

                                                                                        


Monday, November 15, 2010

LAJNAR ISLAMIYYU KARKASHIN HARKAR MUSULUNCI TA GABATAR DA ADDU'AR KWANA ARBA'IN DA RASUWAR MALAM ISHAQ RAFIN DADI

Daga: AbdulAzizi

Lajnar Madarisil Islamiyyah tahti Harakatil Islamiyya ta da'irar Katsina ta shirya tare da gudanar da tunawa da kwana arb'in da rasuwar Malam Ishaq Rafin dadi Katsina da yammacin ranar Talata 3/ 12/ 1431.

Da yake gabatar da takaitaccen jawabi a gaban kabarin Malam Ishaq, Malam Shehu Dalhatu Karkarku wanda ya wakilci Malam Yakubu Yahaya wakilin 'yanuwa almajiran Malam Zakzaky(H) na Katsina, ya fara ne da gabatar da sakon Malam yakubu, inda ya ce,"Malam Yakubu din yana jaddada ta'aziyyarsa ga 'ya'ya , 'yanuwa da almajiran Malam Ishaq gami da mika wannan ta'ziyya ga 'yanuwa almajiran Malam Zakzaky(H) dangane da wannan babban rashi da mukayi" Malam Shehu wanda ya bayyana cewa Malam Yakubu ya yi gurin ya kasance da shi ne ake gabatar da wannan tunawa da rasauwar wannan bawan Allah ,amma saboda kasantuwar ya yi tafiya bai sami damar kasancewa a wannan muhalli ba.

Malam Shehu Ya bayyana cewa Hakika Allah ya karbi rayuwar Malam Ishaq a daidai lokacin da al'umma ke da bukatuwa zuwa ga shiryarwarsa wanda ya dake akan gaskiya duk da tsangwama da yayi ta fuskanta, amma ya dake har Allah ya tabbatar da dugadugansa kamar yadda muka gani. Malam Shehu ya ce, ba shi kadai yake kwance a wannan wuri ba,amma ga shi Allah ya taro masa zukatan Muminai masu kuka dangane da rasa shi, suka baro wuraren ayyukansu suka kawo masa wannan ziyara ta kwana arba'in domin tunawa duk dai albarkacin kiran da Malam din yake yi duk dawannan tsangwama da ya hadu da ita domin raya al'amarin Addini.Sai ya bayyna wannan rasuwa ta Malam Ishaq da cewa, :tunatarwa ce, "ya rage ga remu da muka saura " sai ya yi kira ga 'yanuwa da su yi shiri domin fuskantar wannan rana ta mutuwa.

Malam Shehu ya kuma yi kira ga Malamai na wannan gari, da su yi koyi da Marigayi Malam Ishaq ta hanyar hada kan almajiransa da sauran Musulmi ba kokarin raba kan su ba.

Malam Abubakar Kofar Durbi wanda ya wakilci Shugaban Lajnar Malam yakubu Idris , ya bayyana cewa makasudin shirya wannan tunawa da rasuwar Malam Ishaq, shine domin tabbatar da zumuncin dake tsakanin Malam da 'yuanuwa. ya bayyana cewa shirya wannan munasaba, an yi ta ne bisa umurnin Malam Yakubu Yahaya wanda ya karfafa akan gabatar da ita domin a hadu a bayyana ayyukan wannan bawan Allah . Ya kara da cewa, an gayyato 'yanuwa 'ya'ya da almajiran Malam Ishaq ne ga mi da shirya wasu addu'o'i da karatun al'Qur'ani mai tsarki tare da gabatar da jawabai da babban dansa da kuma almajirinsa hada da Wakilin Malam Yakubu Yahaya zasu gabatar da daren na wannan rana ta Talata domin a bayyana ma jama'a irin gudun muwar da yake bayarwa wajen amsa kiran hadin kan musulmi da Malam Zakaky(H ) yake jagoranta a wannan nahiya., musamman ganin shi kadai ne wanda ya yi fice wajen karba kiran hadin kai da ake yi duk lokacin Mauludin Annabi(SAW) a duk shekara.

A Jawaban da aka gabatar da dare, Manyan almajiran Marigayi Malam Ishaq suka gabatar da jawabai a takaice kan yanda Malam din ya yi kokarin ganin ya koyar da su al'amurra na addini da dama, ciki kuwa har da nuna kauna ga Manzon Allah wanda dama shine abinda Malam Ishaq ya yi fice aka kuma sanshi akan haka.

Malam Ishaq ya yi fice wajen karba kiran makon hadin kai da harkar musulunci ki gabatarwa a duk shekara, shine Malami kwara daya da baya tsoron nuna goyon bayansa ga kiran Malam Duk da cecekucen da yake gamnuwa da shi a tsakanin Malaman garin Katsina akan yadda yake gwamatsar almajiran Malam Zakzaky(H). Taron kareshe da ya halarta na makon hadin kai da Da'irar Katsina ta shirya a mauludin da ya gabata , ya nuna a wajen cewa, babu wani abin da zaya hana shi halartar taron nuna mauludin Manzon Allah, gami da sauran jawabai da ya yi masu matukar gamsarwa da sallamawa ga kiran Malam(H).

Malam Ishaq ya rasu a yanayin da duk wani mumini yake fatan ya yi irin wannan rasuwa, ya rasu a daren Juma'a kuma yana kalmar shahada tare da girmama Allha madaukakin sarki.

Al'ummar da suka hadu wajen wannan zikira duk sun kasance cikin wani yanayi na damuwa da juyayin tunawa da wannan bawan Allah. An yi addu'o'in fatan Allah ta'ala ya tabbatar da kyakkyawan fatan da Muminai suke yi akan sa, da fatan kara gabatar masa da karin adduar nema kasancewa tare da Manzon Allah(SAW) wanda Malamin ya yi suna waje gaba da duk wanda ya kuskura ya yi sakin baki a kan Mauludin haifuwarsa.


Thursday, October 28, 2010

AN GABATAR DA WA'AZIN GORON SALLAH A ZANGON ALARAMMA


Daga: Abdul'Hamid Sani Ilya

Ranar Asabar 9 ga Shawwal, 1431 da yamma `yan uwa Musulmi almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na garin Zangon Alaramma da ke kusa da garin Tsakatsa a Charanci jihar Katsina suka gabatar da Wa’azin goron Salla a garin Zango.
Wanda ya gabatar da Wa’azin a garin ga dimbin al’ummar Musulmin da suka taru don sauraren, shine Wakilin ‘Yanuwa almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na yankin Ganuwa, Rawayau da Kewaye,watau Malam Abdulhamid Iliya Ganuwa.
Malamin ya yi kira ga al’ummar Musulmi da cewa, “Lalle ya kamata mu tuna da makasudin abin da ya sa Allah Ya halicce mu, kuma Ya kawo mu wannan Duniyar da muke rayuwa a cikinta, wadda ko ba-dade ko ba-jima zuwa gare shi zamu koma ko mun so ko mun ki”.
Ya kara da cewa, “A she, in kuwa haka ne, ya zama wajibi a gare mu, musamman mu Musulmi, musan yadda zamu bautawa Allah Madaukkin Sarki ta hanyar bin dokokinsa wadanda ya aiko Manzonsa, Annabi Muhammadu (S) da su zuwa ga bayinsa don mu samu tsira  da kyakkyawan sakamako a wurin Allah ya yin da muka koma zuwa gare Shi a gobe Lahira.”
Sannan Malam Abdulhamid ya karanto ayar nan ta cikin AlKur’ani mai girma wadda Allah Ta’alah ke cewa, “Kuma ban halitta Aljannu da Mutane ba sai domin su bauta mani.” Sai Malam Abdulhamid ya ce, “Hakika wannan ayar ta na nuna mana makasudin abin da ya sa Allah Ta’alah Ya halicci Aljannu da Mutane.”
Kuma ya ci gaba da cewa, “Don haka ba wanda ya cancanci a bautamawa in ba Allah Madaukakin Sarki ba! Kuma wannan shine abin da Allah Ya ke ummurtarmu da shi  a waccan ayar ta Alkur’ani mai girma.
Malam Abdulhamid ya ci gaba da cewa, “In ko muna san musan yadda Allah Ta’alah Ke son a bauta masa, ya zama ba makawa gare mu dole sai mun komawa bin dokokin Allah Ta’alah kai tsaye in har muna son mu fassara waccan ayar da aikata ta a aikace yadda Allah (SWT) Ke so.”
Ya kara da cewa, “ Saboda haka wajibin mu ne mu bi koyarwar Manzon Allah, Annabi Muhammadu (S) da kuma koyarwar Iyalan gidansa tsarkaka, ma’asumai in har muna son musan yadda Allah Ta’alah ke son a bauta masa don mu samu tsira a Lahira! “Wannan kuma shine kiran da Maulana, Mujaddadi, Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya kwashe sama da shekara talatin ya na yi wa bayin Allah da ke wannan nahiya bayani domin mu koma wa bin tsarin dokokin Allah (SWT) in har mu na son mu samu tsira daga azaba a gobe lahira.”

Malam Abdulhamid ya ce, “Godiya da yabo sun tabbata ga Allah Madaukkian Sarki da Ya fahimtar da mu wannan kiran na a komawa tsarin Allah da dokokinsa da Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ke yi a halin da ake ciki yanzu. Tare da fatar Allah Ya amfanar da mu abin da muka ji, Ya kuma ba mu ikon aikatawa.”