Lajnar Madarisil Islamiyyah tahti Harakatil Islamiyya ta da'irar Katsina ta shirya tare da gudanar da tunawa da kwana arb'in da rasuwar Malam Ishaq Rafin dadi Katsina da yammacin ranar Talata 3/ 12/ 1431.
Da yake gabatar da takaitaccen jawabi a gaban kabarin Malam Ishaq, Malam Shehu Dalhatu Karkarku wanda ya wakilci Malam Yakubu Yahaya wakilin 'yanuwa almajiran Malam Zakzaky(H) na Katsina, ya fara ne da gabatar da sakon Malam yakubu, inda ya ce,"Malam Yakubu din yana jaddada ta'aziyyarsa ga 'ya'ya , 'yanuwa da almajiran Malam Ishaq gami da mika wannan ta'ziyya ga 'yanuwa almajiran Malam Zakzaky(H) dangane da wannan babban rashi da mukayi" Malam Shehu wanda ya bayyana cewa Malam Yakubu ya yi gurin ya kasance da shi ne ake gabatar da wannan tunawa da rasauwar wannan bawan Allah ,amma saboda kasantuwar ya yi tafiya bai sami damar kasancewa a wannan muhalli ba.
Malam Shehu Ya bayyana cewa Hakika Allah ya karbi rayuwar Malam Ishaq a daidai lokacin da al'umma ke da bukatuwa zuwa ga shiryarwarsa wanda ya dake akan gaskiya duk da tsangwama da yayi ta fuskanta, amma ya dake har Allah ya tabbatar da dugadugansa kamar yadda muka gani. Malam Shehu ya ce, ba shi kadai yake kwance a wannan wuri ba,amma ga shi Allah ya taro masa zukatan Muminai masu kuka dangane da rasa shi, suka baro wuraren ayyukansu suka kawo masa wannan ziyara ta kwana arba'in domin tunawa duk dai albarkacin kiran da Malam din yake yi duk dawannan tsangwama da ya hadu da ita domin raya al'amarin Addini.Sai ya bayyna wannan rasuwa ta Malam Ishaq da cewa, :tunatarwa ce, "ya rage ga remu da muka saura " sai ya yi kira ga 'yanuwa da su yi shiri domin fuskantar wannan rana ta mutuwa.
Malam Shehu ya kuma yi kira ga Malamai na wannan gari, da su yi koyi da Marigayi Malam Ishaq ta hanyar hada kan almajiransa da sauran Musulmi ba kokarin raba kan su ba.
Malam Abubakar Kofar Durbi wanda ya wakilci Shugaban Lajnar Malam yakubu Idris , ya bayyana cewa makasudin shirya wannan tunawa da rasuwar Malam Ishaq, shine domin tabbatar da zumuncin dake tsakanin Malam da 'yuanuwa. ya bayyana cewa shirya wannan munasaba, an yi ta ne bisa umurnin Malam Yakubu Yahaya wanda ya karfafa akan gabatar da ita domin a hadu a bayyana ayyukan wannan bawan Allah . Ya kara da cewa, an gayyato 'yanuwa 'ya'ya da almajiran Malam Ishaq ne ga mi da shirya wasu addu'o'i da karatun al'Qur'ani mai tsarki tare da gabatar da jawabai da babban dansa da kuma almajirinsa hada da Wakilin Malam Yakubu Yahaya zasu gabatar da daren na wannan rana ta Talata domin a bayyana ma jama'a irin gudun muwar da yake bayarwa wajen amsa kiran hadin kan musulmi da Malam Zakaky(H ) yake jagoranta a wannan nahiya., musamman ganin shi kadai ne wanda ya yi fice wajen karba kiran hadin kai da ake yi duk lokacin Mauludin Annabi(SAW) a duk shekara.
A Jawaban da aka gabatar da dare, Manyan almajiran Marigayi Malam Ishaq suka gabatar da jawabai a takaice kan yanda Malam din ya yi kokarin ganin ya koyar da su al'amurra na addini da dama, ciki kuwa har da nuna kauna ga Manzon Allah wanda dama shine abinda Malam Ishaq ya yi fice aka kuma sanshi akan haka.
Malam Ishaq ya yi fice wajen karba kiran makon hadin kai da harkar musulunci ki gabatarwa a duk shekara, shine Malami kwara daya da baya tsoron nuna goyon bayansa ga kiran Malam Duk da cecekucen da yake gamnuwa da shi a tsakanin Malaman garin Katsina akan yadda yake gwamatsar almajiran Malam Zakzaky(H). Taron kareshe da ya halarta na makon hadin kai da Da'irar Katsina ta shirya a mauludin da ya gabata , ya nuna a wajen cewa, babu wani abin da zaya hana shi halartar taron nuna mauludin Manzon Allah, gami da sauran jawabai da ya yi masu matukar gamsarwa da sallamawa ga kiran Malam(H).
Malam Ishaq ya rasu a yanayin da duk wani mumini yake fatan ya yi irin wannan rasuwa, ya rasu a daren Juma'a kuma yana kalmar shahada tare da girmama Allha madaukakin sarki.
Al'ummar da suka hadu wajen wannan zikira duk sun kasance cikin wani yanayi na damuwa da juyayin tunawa da wannan bawan Allah. An yi addu'o'in fatan Allah ta'ala ya tabbatar da kyakkyawan fatan da Muminai suke yi akan sa, da fatan kara gabatar masa da karin adduar nema kasancewa tare da Manzon Allah(SAW) wanda Malamin ya yi suna waje gaba da duk wanda ya kuskura ya yi sakin baki a kan Mauludin haifuwarsa.
Allah madaukakin nSarki ya gafarta ma Mal. Ishaq ya sa muma mu cika da Imani.
ReplyDelete