Friday, November 26, 2010

YADDA DA'IRAR KATSINA TA GABATAR DA IDIL GADEER A SHEKARAR 1431

Daga: Abdulazizi / Zaharadden
                                                                        
                
A ranar Juma'a 20 ga watan Zul-Hijja  1431 Hijiriyyah, wanda ya zo daidai da 26 / 11/ 2010 Miladiyyah, Da'irar 'yanuwa Musulmi almajiran Sayyeed Ibrahim Zakzaky(H) ta katsina ta gabatar da taron wa'azin murnar Idil Gadeer na wannan Shekara ta 1431, a harabar masallacin Juma'a dake cikin birnin Katsina.
Taron wanda ya fara da misalin karfe hudu da rabi na yammacin ranar ta Juma'a, an bude shi ne da karanto wasu daga cikin ayoyin al-Qur'ani mai tsarki da ga bakin dan uwa Malam Adamu Gobarau. Bayan sa ne sai Malam Sabo ATC ya gabatar da 'yan wasan kwaikwayo na Dan Fodiyo, inda Malam Ahmad Kofar Sauri ya jagoranci gabatar da 'yanwasan, inda suka gabatar da wata Tamsiliyya mai kayatarwa mai suna "CIN AMANA". tamsiliyyar ta yi nuni ne da abubuwan da suka faru a tarihi na canja wakilcin da Manzon Allah (SAWW) ya yi, tare da kawo wasu abubuwa da suka shafi hana Sayyida  Zahara(AS) gadonta gami da zuwa gidanta da aka yi aka banka kyauren da ya yi sanadiyyar zubewar cikin da take dauke da shi Na Muhsin da kuma yin sanadiyyar Shahadarta daga bisani. Masu gabatar da tammsiliyyar sun yi kokarin isar da sakon nasu cikin hikima tare da sakaya sunayen duk masu hannu a afkar da wannan waki'a.

Daga nan ne sai aka ba mawakan gwagwarmaya dama suma suka bada tasu gudunmuwa ta hanyar wake Imam Ali Zakin Allah.(AS).
Wanda ya gabatar da jawabi a wannan taro shi ne Malam Shehu Usman Dalhatu  Karkarku a madadin Malam Yakubu Yahaya. Mal Shehu ya bayyana cewa Wannan Munasaba ta Gadeer ,Munasaba ce da ta shafi dukkan Musulmi ba 'yan shi'a ba. Munasaba ce wadda Manzon Allah ya kama hanun ImamAli(AS) ya daga sama, sannan ya ce "wanda na kasance Shugabansa, to ga Ali nan shine Shugabansa" san ya yi Addu'a da cewa"Allah ka taimaki wanda ya taimake shi, ka kuma watsar da wanda ya watsar da shi" . Sanna sai ya jawo hankalin Musulmi da cewa, wannan al'amari ba siyasa bace kamar yadda wasu suke gani, a'a addini ne. Malamin ya ce ,ko da yake bayan Manzon ya yi wafati,wasu sun sun canja sun zabi na su shugaba. Saannan sai ya yi tambaya ga masu ganin 'yan shi'a basu yarda da wannan canji ba da wasu suka yi akan na Manzo da cewa, wasu Sahabban suma  basu yi bai'a ba ga wannan canji, su ya ya zaka ce masu?
da ya juya kan yadda aka kirkiro Hadisai na karya, irin masu nuna cewa' wai Manzo ya ce" abi shugaba, na kirki ne ko  fajiri" sai ya ce irin wadannan Hadisai ne suka sa musulmi suke bin Fajiran shugabanni abinda ya kai su ga bin jagorancin kafirin Shugaba. Sannan yace " idan ka damfara jagorancinka ga wanda ba Manzo ne ya ayyana shi ba, to bai yi daidai ba"

Sannan ya jawo hankalin al'umma da cewa Manzo ya yi umurnin Duk wanda ya ji wannan sako , ya isar da shi ga  wanda bai ji ba, Uba ya isar ma da 'ya'yansa, 
A karshe ya bayyana cewa, idan har addini ba shi da jagoranci iriin wanda Manzo ya kafa, to dole ne za a ci gaba da zama cikin rigingimu, kuima idan ka rasa jagorancin Imam Ali (AS) zaka ci gaba da zama karklashin jagorancin Fajirai.
 Ya yi fatan Allah (T) ya amsa mana wannan Wila'a da  muka yi ga Imam Ali (AS) a karkashin jagorancin Sayyeed Zakzaky(H).


Wani bangare na 'yanuwa suna sauraren jawabin da Malam Shehu Karkarku ya gabatar a wajen taron Gadeer da Da'irar Katsina ta gabatarta


'Yanuwa mata suna sauraren jawabin Gadeer da aka gabatar a Katsina

                                                                                        


No comments:

Post a Comment