Sunday, June 10, 2012

ACADAMIC FORUM YANKIN KATSINA YA GABATAR DA TARON MAKON IMAM KHUMEINE(KS) NA WANNAN SHEKARA TA 2012



Aranar Lahadi 10/ 6/ 2012 , dandalin dalibai na Acadamic Forum yankin Katsina ya gabatar da taron tunawa da makon Imam khomene (KS) na wannan shekara a dakin taro na ‘women centre’ dake unguwar  filin samji Katsina.

A jawabin da ya gabatar, Shekh Muhammad Mahmud Turi, wakilin Sayyid  Ibrahim Yakubu Zakzaky(H) a birnin Kano , ya karanto kadan daga tarihin Marigayi Imam Khumene(KS). Malam Turi ya bayyayana cewa, Imam ya  taso ne a gidan Ilimi, amma a yanayi na maraici domin mahaifansa sun rasu tun yana karami,amma a haka ya yi  ta rayuwa irin ta neman ilimi ya kuma rayu a cikin yanayi  karancin abin hannu domin an tabbatar da cewa, a lokacin bargo daya ne kadai ya mallaka, amma a haka ya ci gaba da neman ilimin.Malamin ya  ce, tun yana da kananaan shekaru ya fara koyarwa a Hauza saboda hazaka da Allah (T) ya  ba shi.Malam Turi ya kara bayyana cewa, Allah madaukakin Sarki ya haska ma  Imam halin da al’ummar iran ta ke ciki na rashin bin dokokin Allah, bayan da Imam ya fara wayar ma al’umma da kai sai gwamnatin Sha, ta yi yunkurin kashe shi, abinda ya sa Malamai suka bayyana Imam khomene a matsayin Ayatul lahi, hakan yasa dole Sarki Sha ya janye yunkurin kasha shi, sai dai gwamnatin ta kore shi daga Iran ,inda ya yi hijira zuwa kasar turkiya sannan daga can zuwa kasar iraki, inda a can din ma dai ya ci gaba da wayar ma al’umma kai musamman abin da ya shafi Fikira akan ‘Wilayatul fakihi’ watau jagorancin Malami, wannan kira na imam ya jawo masa kyama daga Malamai.
malam Turi ya kara da cewa, duk lokacin da Musulmi suka yi watsi da tsarin Allah, to rayuwarsu zata kasance a cikin kaskanci, kamar abinda yake faruwa a wannan kasa a halin yanzu. Ya ce, Imam ya ci gaba da kokarin wayar ma mutane kai akan  hadarin bin tsarin gwamnatin da bata musulunci ba domin rashinta gwamnatin musulunci na hana aikatuwar musuluncin. Malam Turi ya kara da cewa, Imam ya yi gwagwarmaya da malamai fiye da yadda ya yi da Kafirai, domoin Malaman suna zarginsa da kawo cikas wajen bayyanar Imam Mahadi(AJ)
Malam Turi ya bayyana wasu darussa da za a dauka a rayuwar wannan bawan Allah inda malamin ya yi tambayar cewa, Mi yasa Imam ya sami wannan nasara , amma ga dimbin Malamai basu sami wannan ba? Sai ya bada amsar cewa, Imam ya na da zuciya daya,sai ya ba Allah(T) wannan zuciya sai Alah ya hore masa zukatan al’umma.  

Malam Turi ya kirayi ‘yanuwa akan yaki da zukata  domin kauce ma abubuwan da za su bata zuciya saboda shagaltar da ita tare da  gurbata ta yadda ba zata iya yunkurin gwagwarmayar  tabbatar da addini ba.
A lokacin da yake kira akan kulawa da tarbiyyar ‘ya’ya, Malam Turi ya bayyana cewa, gurin makiyanmu shi ne  su bata tarbiyyar  musulmi, sai ya bayyana muhimmancin kulawa da  tarbiyyar yara domin su kasance sun sami tarbiyyar addini domin su zamo cikin rundunar da zata zamo ta Allah. Da zata taimakama addini.
A wani bangaren jawabin nasa, ya bayyana cewa, duk jama’ar da tadanfaru da Imam Khomenei, za a ga bambanci da sauran  koda kuwa Shi’a mutum ya ke yi.Ya bada misalin wasu kasahe irin su Pakistan da suke da Shi’a, amma saboda basu damfare da Imam basu sami daukaka ba, amma ga Hizbullahi nan yadda suka buwaya.
A karshe ya bayyana cewa, a wannan kasa babu mafita ga al’umma sai ta hannun Mujaddadin wannan al’umma  Sayyid Zakzaky(H) kamar yadda shehu Usman dan Fodiyo ya  yi bushara.’abinda ya kamace mu shi ne riko da wannan gwagwarmaya ta hanyar kyautata alaka da Allah kamar yadda Sayyid Zakzaky(H) ya ke kira akai’

Saturday, June 2, 2012

DANDALIN MATASA NA HARKAR MUSULUNCI A NIJERIYA YANKIN KATSINA YA GABATAR DA MAULUDIN FATIMA(AS) A GARIN KANKIA, JIHAR KATSINA


Zama matashi mai addini babban matsayi  ne, kuma falala ce daga Allah(T). Malam Yakubu Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabin mauludin Syyida Azzahara(AS) da dandalin matasan harkar musulunci karkashin jagorancin Sayyid  Zakzaky(H) na yankin da’irar Katsina da kewaye ya shirya ya kuma  gabatar a dakin taro  na ‘Shema youth empowerment  Centre’ dake garin Kankia, jihar Katsina, a ranar Lahadi  7 /7/1433.

Malam Yakubu  ya ci gaba da cewa, duniya gaba dayanta, a wannan lokaci matasa ne suke tafiyar da ita, ina ya bada misali da manyan kasashen  duniya  dama wannan kasa da cewa,shugabanninsu duk matasa ne, haka idan aka dubi rundunonin soji  da sauran jami’an  tsaro na duniya, duk za a ga dai matasa ne  suke jagorantar su, ya ce, duk wasu bangarorin tafiyar da al’amurran al’umma dai zaka ga cewa,matasane ke rike da su. Ya ce, hakama  lamarin Lahira ta matasance,inda  ya bayyana Imam Hasan da Husaini (AS) a matsayin shugabannin aljanna. ya kuma karanto kissar Annabawan Allah da suka hada da Annabi Ibrahim da sauransu da irin gwagwarmayarsu da zalunci duk suna matsayin matsa ne suka aiwsatar da haka. Sannan  idan aka dubi ashabul  Kahfi  suma matasanne,ya ce, wadanda suka rufa ma Manzo baya a lokacin kiransa irinsu Imam Ali ,Sayyida Zahara(AS)  da sauran su  ,za a ga cewa dai matasan ne.ya kara da cewa, haka ma Mujaddadai  irinsu Shehu dan Fodiyu Da Imam Khomenei (KS) duk matasa ne suka dafa masu sai ya ce duk wannan yana nuna maka cewa,matasa sune  jari na duniya da Lahira, kuma akan yarinta ake gina duniya da Lahira,ya kara bayyana cewa, “ba girman jiki bane , zuciya ce mai kyau da ta  siffantu da ibada.” sai  ya ankarar da matasa akan yunkurin da makiya suke yi na  rosa tarbiyyarsusannan ya   nuna wajabcin lura tare  da kauce ma afkawa cikin hadartin wannan tarko. Sai ya bayyana mafita daga wannan tarko da cewa, itace addini ,”a dasa ma matashi tsoron Allah, ibada da son  Lahira tare da tsaron azabarta ,”kuma wannan shi ne manufar kiran Sayyid  Zakzaky(H) ,  ba  al’amarin neman mukamin duniya ba ne”,
Ta bangaren Sayyida Zahara(AS) kuwa, Malam Yakubu ya tabo wasu kadan daga matsayai  da falalolin da Allah ya bata Musamman Tsayuwarta dadagewarta akan bin Allah da taimaka ma sakon da aka aiko Manzo  Da shi,sannan ya bayyana  cewa, al’amarin ahlul Bayt abu ne  mai hatsari domin kuwa abu ne wanda ya shafi Imani.Ya kara da cewa,zaka ga mutum ya yi imani da sakon Manzo a dunkule , amma  da an ce ayi dalla-dalla sai ka ga yana shafa keya bai yarda ba. Ya tabo abubuwa da dama  da suka shafi  hakkkin ahlul Bayt da suka hada da Khumusi,Wila’a  da jagorancin su  kamar maganar  ‘ Halifofi bayana Sha biyu ne” kamar  yadda yake a littafan Buhari da MUsulimu, amma dai mutane  ba su yarda ba, inda zaka ga babban Malami idan aka yi masa wannan bayani baya yarda, haka kuma yake ga sauran musulmin duniya. Sai ya yi mamakin yadda kiriri aka maida Halifofin Annabi  guda Hudu, bayan shi Annabin ya ce Sha biyu ne kamar yadda ya zo a Buhari da Muslim,  ya ce “lallai akwai hadari akan wannan” ya kammala da cewa, ” Ba so bane kawai, a‘a  bi ne ga wadannan  bayin Allah” 




Tuesday, May 15, 2012

MUZAHARAR MAULUDIN SAYYIDA FATIMA AZZAHARA (AS) A KATSINA




‘yayanuwa mata almajiran Sayyid Ibarahim Zakzaky(H) dake  da’irar  Katsina, sun shirya  tare da gabatar da  muzaharar  mauludin Sayyida  Fatima azzhara diyar Manzon Allah (S) ta wannan shekara a wannan rana ta Talata,24/6/  1433 
.
Muzaharar  wadda  aka soma da misalin karfe tara da rabi na safiyar  wannan  rana , ta sami halartar ‘yanuwa  mata  daga yankuna  daban-daban na cikin garin Katsina  da kewaye, a  bisa      rakiyar Harisawa  da  suke a goshin wannan muzahara , sannan ‘yan makarantun Islamiyyu na ciki da wajen garin  Katsina da suke dauke da tutoci iri daban-daban  ana tafe mawakan Harkar musulunci na rero baitocin  yabo ga Sayyida Fatima(AS)  dama wakokin mahaifin ta da sauran “ya’yanta  A’immatul huda(AS).
Muzaharar  wadda  ta zagaye  muhimman  titunan garin Katsina, ta kayatar ainun ida aka kwatanta ta da wadanda suka gabace ta, duk da karacin abubuwa kamar yadda daya daga cikin masu shirya ta  ta shaida ma  manema  labarai da suka zanta da ita. Malam Bilkisu idris  ta ce, “akwai shirye-shirye da  za a gabatar idan Allah ya nuna mana ta shekara mai zuwa, wanda ta ce, za su fadada shirin domin gayyato mata daga bangarori da yawa na cikin garin Katsina.
A jawabin da ta gabatar bayan kammala wannan muzahar, Malama Safiya Kabir, ta bayyana  wasu kadan daga cikin matsayai  na wannan  baiwar Allah da cewa, ita  ce wadda Allah da kansa ya daura mata aure da babban bawansa Imam Ali (AS), sannan ta bayyana takaicin irin wahalhalu da wannan baiwar Allah ta hadu da su tun bayan wafatin mahaifinta  Annabi  Muhammad (S).Ta ce, a yunkurin rufe matsayi  da darajarta  ne,  ba za ka taba jin ana karanto wasu Hadisai da za a danganta ruwayarsu daga wajen ta ba, domin  kada jama’a  su fahinci wasicin da Annabi ya yi  na bain  shiriya a hannun jikokinta, sai tayi  fatan al’umma  musamman ‘yanuwa  mata  za su yi bita akan rayuwarta su kuma yi koyi da halaye irin na Fadima(AS).
Kafin wannan muzahar, sai da kwamitin ‘yanuwan mata ya gabatar da wata ziyara zuwa ga malaman makarantun  allo dake yankuna  hudu na bangarorin da ake da su  a wannan  da’ira  da suka hada da yankunan  Gabas, Yamma, Kudu da kuma Arewa  wtau  (Zones) tare da gabatar ma almajirai da malamansu  kyaututtuka  na  abinci  da kuma sabulan wanki albarkacin wannan baiwar Allah .
Za dai aci gaba da gabatr da wannan gagarumin biki na tuna haifuwar diyar Manzon Allah Fatima azzhara (AS)  a rana daya da ta rage  inda Malam Yakubu Yahaya zaya gabatar da jawabin karshe na wannan biki.


Sunday, May 6, 2012

A KARO NA UKU: AN TUNA DA SHAHADAR ALHAJI IBRAHIM HAMDALA CHARANCI


A karo na uku, Mu’assasatus shuhada  da   bangaren ‘yanuwa na kwamitin ahl-duthour  yankin da’irar Katsina, suka gabatar da taron tunawa da shahadar  Alhaji Ibrahim  hamdala  Charanci  dake  jihar  Katsina  da yammacin ranar Assabat 14/6/1433.
 A jawabin da ya gabatar, Malam  Shehu  Dalhatu  Karkarku, ya bayyana Shahada  da cewa falala  ce da Allah (T) yake  bayar da ita ga daidaikun bayinsa musamman a irin wannan lokaci da al’umma bata  bisa tsarin  Allah. Malam Shehu Dalhatu ya bayyana matakai  da Shehu Usmanu  Mujaddadi  ya  bayyana da suka wajaba musulmi su dauka  a duk lokacin  da suka  sami  kansu a wurin da ba  a bin dokokin Allah, wadannan  abubuwa  kuwa  sune, kauracewa  daga wannan wuri  da ya  bijire  ma tsarin  Allah, ko kuma gwagwarmayar  tabbatar  da tsarin  Allah din  ko  kuma mutum  ya tafi daji ya sami wata itaciya ya ciza har sai ya mutu.
Ya yi tir da  yadda  ake  ta yunkurin  bata  kiran komawa  ga tsarin Allah  da sukar kiran da sunan ana shi’a, wai kuma shi’ar  ba addini ba ne. Yace, “amma kiran shi ne mafita ga al’umma  daga wannan yanayi  na zalunci da ake ciki” daga nan Malam Shehu ya gutsuro matsayin shahidi da bayyana kadan daga  cikin matsayan da suka hada da , ceton mutane  saba’in  daga cikin danginsa,  bayan  rahama da yake  cikinta  tun kafin tashin kiyama. Ga makasan Alhaji Ibrahim kuwa,  ya bayyana matsayinsu ne na dawwama cikin azabar wuta  kamar yadda Allah(T) ya fada a cikin littafinsa mai tsarki.
A tun farko sai da aka gabatar da ziyarar Shahidin a makwancinsa, inda Malam Muhammad Awwal  Iyal Zariya  ya gabatar da takaitaccen jawabin da a cikinsa ya tunatar akan irin ta’addancin da aka yi ma Alhaji Ibrahim  na kisan gilla ba domin komi ba  sai dai saboda imaninsa. Ya  kawo misalin halin da al’umma take  ciki na zalunci da kashe-kashe  da ake ta yi  akan musulmi, inda ya bayyana mafita daga wannan yanayi  sa cewa, ita ce, matsayar da Imamu Husaini(AS) ya dauka a lokacin da ya ga addinin Manzon Allah  yana fuskantar  rusawa, abinda ya kai ga shahadarsa .malam Awwal ya kara da cewa, gwagwarmaya a irin wannan lokaci ita ce kawai mafita, ya yi nuni da cewa, ko a kasashe irin su Iraki da  Amerika  ta kai mamaya  tana kashe  jama’ar  kasar, g wagwarmaya  suka yi  har sai da Amurka din ta ga babu wurin zama sannan ta fara janye sojojinta  daga kasar. Sai ya ce a wannan  kasar ma gwagwarmaya  karkashin jagorancin  Sayyid Zakzaky(H) tare  da  tsayuwa  akan tafarki  ne  kadai zaya kawo  mafita ma wannan al’umma .
Idan za a iya tunawa, kimanin shekaru uku  da suka gabata ne,  wasu  gungun ‘yan ta’adda  suka kai ma shahid  Alhaji  Ibarahim Hamdala hari a gidansa bayan ya tashi daga shagonsa, inda suka sassare shi har suka shahadantar da shi.
‘Yanuwa daga garuruwa da dama  ne suka sami halartar wannan tunawa  da shahadar  tasa.  




Sunday, April 22, 2012

MU'ASSASATUS SHUAHADA'U TA GABATAR DA TARON KARA MA JUNA SANI NA WUNI UKU A KATSINA







A karo na biyar, Mu’assasatus Shuhada’u a Harkar musulunci a  Najeriya  da Sayyid Ibrahim Zazaky(H)     yake yi ma jagoranci, ta shirya taron karama juna sani  na ‘ya’yan Shahidan Harkar wanda yankin Shahid Hamza da ke KAtsina  ya shirya  a  garin  tun daga ranar Juma’a  29/5/ ha r  zuwa 1/6/ 1433.
A jawaban da  aka gabatar da suka kunshi muhadarori da masu jawabai . Dokta Abdullahi  Dan Ladi wanda ya yi jawabi aklan ‘ Ilimi ginshikin rayuwa” ya  bayyana  ilimin  da cewa, haske ne da Allah yake jefa shi a cikin zuciyar wanda ya ga dama, inda  ya  bayyana cewa, kowace halitta da Allah ya samar, to tana da nata ilimi da aka kimsa mata sai dai ilimin yakan bambanta  da na  juna. Dokta Abdullahi  ya bayar da misalai akan halittu na dabbobi da yadda suke rayuwa a tsakaninsu  abisa  ilimi  da Allah  ya hore masu, sai  ya  ce  amma ilimi dan  Adam ya bambanta dana dabba.
Dangane da ilimin Dan Adam,  cewa  ya yi,akwai wanda  mutum  ya  gada  kuma  yake koyo acikin al’uimmar da yake rayuwa  a cikinta sannan wanda ake koyowa a hannun malamai.
Dokta  ya  bayyana cewa, rayuwar mutum bata takaita anan duniya ba, akwai wata rayuwar ta bayan mutuwa, sai  ya ce, duk  wanda aka halitta , to za a yi masa Hisabi, kuma  ana  yi ma mutum  Hisabinne gwargwadon Iliminsa , ya bayyana  cewa, sai mutum  ya san Mahaliccinsa  sannan ne zaya iya bauta masa yadda ya kamata, sannan dole aikin mutum ya tafi kafada da kafada da iliminsa. Sai ya bayyana ilimin boko da cewa da shi da na addini duk daya ne matukar dai mutum ya yi  ilimin  domin Allah  da kuma niyyar taimakama al’umma. Ya kara da cewa, kamar yadda za a iya yi ma mutum azaba akan ilimin boko, to haka ma za a iya yin azabar ga mai ilimin addini madamar mai na  addini  bai yi amfani da ilimin  ba. Sai ya bayyana al’amarin karatu da cewa, ba abune mai sauki ba sai an dage sannan ne ake samunsa. Sai ya bukaci ‘ya’yan Shahidan da su  dage su kokarta su taka duk wani fage na ilimi da ake da shi, kuma a shirye Mu’assasar  take ta dauki  nauyin duk dan Shahidin da ya sami damar kara karatu kowane iri ne .
A jawabin da ya gabatar  Malam Abdull Hamid Bello Shugaban wannan Mu’assasa ta Shahidan Harkar musulunci, ya yi Magana ne akan kyawawan dabi’u, inda ya karanto Hadisai masu dama da suke Magana akan matsayin dabvi’u masu kyawu. Malam Abdul Hamid ya bayyana  tarbiyya   da cewa, ita ce,yin aiki mai kyau da barin maras kyau” Sannan ya bayyana cewa, Allah ya aiko mana da abin koyi watau Manzon Allah (S) wanda yake rahama a cikin halittu,sannan wannan Manzo shine madubi  da zamu kalla domin koyon dabi’u  daga wajen sa.Sai ya bukaci mahalarta da su siffantu da duk dabi’u  kyawawa  na  addini kamar ,gaskiya ,hakuri, yakini akan abinda mutum yake yi ,kyauta da dabi’ar mutunta kai”muru’a”ya kuma bukaci mahalarta su yi dubi cikin lamurransu domin siffantuwa da irin wadannan dabi’u saboda da irinsu ne kawai za a iya kawo gyara a cikin al’umma..
A jawabin kammal  wannan taro da ya  gabatar,  Malam Yakubu Yahaya  ya fara ne da gode ma Allah (T) da ya hukumta yin wannan taro na ‘ya’yan Shahidai masu albarka  a wannan Gari na Katsina,sai ya bayyana Shahada da cewa, ita ce sirrin nasara ”bama addini ba har lamurran rayuwa  ana bukatar sadaukarwa inada ya nusar  ta hanyar kawo wasu misalan al’ummu da suka sadaukar domin  su kubutar da kansu daga danniyar ‘yan mulkin mallaka inda  ya bayar da misalin gwagwarmayar mutanen Kenya da Aljeriya  a yayin kwatar kansu daga Turawa,sannan ya ce. Gwargwadon  sadaukarwarmu, daidai nasara da zamu samu sai ya nuna muhimmancin mu kara sadaukarwa  akan wannan tafarki na Addini” yadda  tarbiyya ta gurbata a wannan al’umma tamu, mafita daga wannan yanayi yana bukatar sadaukarwa”. Malam Yakubu  ya ce, Allah ya yi mana baiwar kasha  99 bisa dari domin ya albarkace  mu da  jagoranci , kuma wannan jagoranci  shi ne  makami na nasar saura kashi  daya  ake bukatar mu aikata, wannan  kashi guda kuma  shi ne “ji da  bi” ga wannan jagora . Malam Yakubun ya jawo hankalin ‘ya’yan Shahidan  da  cewa, su tsayu akan abinda  iyayensu suka sadaukar da rayuwarsun akansa watau gwagwarmayar addini sannan su guji aikata duk abinda za ya bakanta ran mahaifansu domin suna kawo masu ziyara lokaci-lokaci kamar yadda ya tabbata a Hadisin Annabi(S) Ya kuma bukaci  masu kula da iyalan shahidan  da s kara u kula da abubuwan da  yaran  su kanyi , a kwabe su idan suka yi abin da bai kamata ba. Ya tsoratar da yaran cewa, su guji yi kahon cewa, su ‘ya’yan sahidai ne  amma  su basu yin aikin da iyayen nasu suka  yi,  inda  ya  ce wannan ba zaya  fitar da su ba a lahira  sai dai idan sun yi aiki na kwarai . ya  kuma ankarar akan al’amarin wayoyin yaran da cewa, akwai  bukatar a rika kulawa da halin da wayoyin yaran suke ciki, domin akwai makircin bata  tarbiyyar ‘ya’yanmu da aka bollo da shi ta hanyar wayoyin tafi da gidanka.
A wannan mu’tamar an  samu nasarar kai ziyarori a wuraren  tarihi  da suka hada da Hasumiyar Gobarau,da Makabartar Dan Marna  wani waliyyi da aka yi  a Katsina  sai zuwa rijiyar  Gusugu dake birnin Daura tare da ziyatar shahid Ibrahim Muhammad Zariya da ya sami shahadarsa a lokacin waki’ar  janar Abacha.
Manufar shirya wannan taro dai  kamar yadda  Malam Abdul Hamid ya bayyana ma almizan shi   ne gina tarbiyyar ‘ya’yan  shahidai  a tafarkin da iyayensu  suka sadaukar da rayukansu  tare da wayar masu da kawunansu akan muhimman wurare na tarihi dake cikin wannan kasa.