Tuesday, May 15, 2012

MUZAHARAR MAULUDIN SAYYIDA FATIMA AZZAHARA (AS) A KATSINA




‘yayanuwa mata almajiran Sayyid Ibarahim Zakzaky(H) dake  da’irar  Katsina, sun shirya  tare da gabatar da  muzaharar  mauludin Sayyida  Fatima azzhara diyar Manzon Allah (S) ta wannan shekara a wannan rana ta Talata,24/6/  1433 
.
Muzaharar  wadda  aka soma da misalin karfe tara da rabi na safiyar  wannan  rana , ta sami halartar ‘yanuwa  mata  daga yankuna  daban-daban na cikin garin Katsina  da kewaye, a  bisa      rakiyar Harisawa  da  suke a goshin wannan muzahara , sannan ‘yan makarantun Islamiyyu na ciki da wajen garin  Katsina da suke dauke da tutoci iri daban-daban  ana tafe mawakan Harkar musulunci na rero baitocin  yabo ga Sayyida Fatima(AS)  dama wakokin mahaifin ta da sauran “ya’yanta  A’immatul huda(AS).
Muzaharar  wadda  ta zagaye  muhimman  titunan garin Katsina, ta kayatar ainun ida aka kwatanta ta da wadanda suka gabace ta, duk da karacin abubuwa kamar yadda daya daga cikin masu shirya ta  ta shaida ma  manema  labarai da suka zanta da ita. Malam Bilkisu idris  ta ce, “akwai shirye-shirye da  za a gabatar idan Allah ya nuna mana ta shekara mai zuwa, wanda ta ce, za su fadada shirin domin gayyato mata daga bangarori da yawa na cikin garin Katsina.
A jawabin da ta gabatar bayan kammala wannan muzahar, Malama Safiya Kabir, ta bayyana  wasu kadan daga cikin matsayai  na wannan  baiwar Allah da cewa, ita  ce wadda Allah da kansa ya daura mata aure da babban bawansa Imam Ali (AS), sannan ta bayyana takaicin irin wahalhalu da wannan baiwar Allah ta hadu da su tun bayan wafatin mahaifinta  Annabi  Muhammad (S).Ta ce, a yunkurin rufe matsayi  da darajarta  ne,  ba za ka taba jin ana karanto wasu Hadisai da za a danganta ruwayarsu daga wajen ta ba, domin  kada jama’a  su fahinci wasicin da Annabi ya yi  na bain  shiriya a hannun jikokinta, sai tayi  fatan al’umma  musamman ‘yanuwa  mata  za su yi bita akan rayuwarta su kuma yi koyi da halaye irin na Fadima(AS).
Kafin wannan muzahar, sai da kwamitin ‘yanuwan mata ya gabatar da wata ziyara zuwa ga malaman makarantun  allo dake yankuna  hudu na bangarorin da ake da su  a wannan  da’ira  da suka hada da yankunan  Gabas, Yamma, Kudu da kuma Arewa  wtau  (Zones) tare da gabatar ma almajirai da malamansu  kyaututtuka  na  abinci  da kuma sabulan wanki albarkacin wannan baiwar Allah .
Za dai aci gaba da gabatr da wannan gagarumin biki na tuna haifuwar diyar Manzon Allah Fatima azzhara (AS)  a rana daya da ta rage  inda Malam Yakubu Yahaya zaya gabatar da jawabin karshe na wannan biki.


No comments:

Post a Comment