Sunday, May 6, 2012

A KARO NA UKU: AN TUNA DA SHAHADAR ALHAJI IBRAHIM HAMDALA CHARANCI


A karo na uku, Mu’assasatus shuhada  da   bangaren ‘yanuwa na kwamitin ahl-duthour  yankin da’irar Katsina, suka gabatar da taron tunawa da shahadar  Alhaji Ibrahim  hamdala  Charanci  dake  jihar  Katsina  da yammacin ranar Assabat 14/6/1433.
 A jawabin da ya gabatar, Malam  Shehu  Dalhatu  Karkarku, ya bayyana Shahada  da cewa falala  ce da Allah (T) yake  bayar da ita ga daidaikun bayinsa musamman a irin wannan lokaci da al’umma bata  bisa tsarin  Allah. Malam Shehu Dalhatu ya bayyana matakai  da Shehu Usmanu  Mujaddadi  ya  bayyana da suka wajaba musulmi su dauka  a duk lokacin  da suka  sami  kansu a wurin da ba  a bin dokokin Allah, wadannan  abubuwa  kuwa  sune, kauracewa  daga wannan wuri  da ya  bijire  ma tsarin  Allah, ko kuma gwagwarmayar  tabbatar  da tsarin  Allah din  ko  kuma mutum  ya tafi daji ya sami wata itaciya ya ciza har sai ya mutu.
Ya yi tir da  yadda  ake  ta yunkurin  bata  kiran komawa  ga tsarin Allah  da sukar kiran da sunan ana shi’a, wai kuma shi’ar  ba addini ba ne. Yace, “amma kiran shi ne mafita ga al’umma  daga wannan yanayi  na zalunci da ake ciki” daga nan Malam Shehu ya gutsuro matsayin shahidi da bayyana kadan daga  cikin matsayan da suka hada da , ceton mutane  saba’in  daga cikin danginsa,  bayan  rahama da yake  cikinta  tun kafin tashin kiyama. Ga makasan Alhaji Ibrahim kuwa,  ya bayyana matsayinsu ne na dawwama cikin azabar wuta  kamar yadda Allah(T) ya fada a cikin littafinsa mai tsarki.
A tun farko sai da aka gabatar da ziyarar Shahidin a makwancinsa, inda Malam Muhammad Awwal  Iyal Zariya  ya gabatar da takaitaccen jawabin da a cikinsa ya tunatar akan irin ta’addancin da aka yi ma Alhaji Ibrahim  na kisan gilla ba domin komi ba  sai dai saboda imaninsa. Ya  kawo misalin halin da al’umma take  ciki na zalunci da kashe-kashe  da ake ta yi  akan musulmi, inda ya bayyana mafita daga wannan yanayi  sa cewa, ita ce, matsayar da Imamu Husaini(AS) ya dauka a lokacin da ya ga addinin Manzon Allah  yana fuskantar  rusawa, abinda ya kai ga shahadarsa .malam Awwal ya kara da cewa, gwagwarmaya a irin wannan lokaci ita ce kawai mafita, ya yi nuni da cewa, ko a kasashe irin su Iraki da  Amerika  ta kai mamaya  tana kashe  jama’ar  kasar, g wagwarmaya  suka yi  har sai da Amurka din ta ga babu wurin zama sannan ta fara janye sojojinta  daga kasar. Sai ya ce a wannan  kasar ma gwagwarmaya  karkashin jagorancin  Sayyid Zakzaky(H) tare  da  tsayuwa  akan tafarki  ne  kadai zaya kawo  mafita ma wannan al’umma .
Idan za a iya tunawa, kimanin shekaru uku  da suka gabata ne,  wasu  gungun ‘yan ta’adda  suka kai ma shahid  Alhaji  Ibarahim Hamdala hari a gidansa bayan ya tashi daga shagonsa, inda suka sassare shi har suka shahadantar da shi.
‘Yanuwa daga garuruwa da dama  ne suka sami halartar wannan tunawa  da shahadar  tasa.  




No comments:

Post a Comment