Saturday, June 2, 2012

DANDALIN MATASA NA HARKAR MUSULUNCI A NIJERIYA YANKIN KATSINA YA GABATAR DA MAULUDIN FATIMA(AS) A GARIN KANKIA, JIHAR KATSINA


Zama matashi mai addini babban matsayi  ne, kuma falala ce daga Allah(T). Malam Yakubu Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabin mauludin Syyida Azzahara(AS) da dandalin matasan harkar musulunci karkashin jagorancin Sayyid  Zakzaky(H) na yankin da’irar Katsina da kewaye ya shirya ya kuma  gabatar a dakin taro  na ‘Shema youth empowerment  Centre’ dake garin Kankia, jihar Katsina, a ranar Lahadi  7 /7/1433.

Malam Yakubu  ya ci gaba da cewa, duniya gaba dayanta, a wannan lokaci matasa ne suke tafiyar da ita, ina ya bada misali da manyan kasashen  duniya  dama wannan kasa da cewa,shugabanninsu duk matasa ne, haka idan aka dubi rundunonin soji  da sauran jami’an  tsaro na duniya, duk za a ga dai matasa ne  suke jagorantar su, ya ce, duk wasu bangarorin tafiyar da al’amurran al’umma dai zaka ga cewa,matasane ke rike da su. Ya ce, hakama  lamarin Lahira ta matasance,inda  ya bayyana Imam Hasan da Husaini (AS) a matsayin shugabannin aljanna. ya kuma karanto kissar Annabawan Allah da suka hada da Annabi Ibrahim da sauransu da irin gwagwarmayarsu da zalunci duk suna matsayin matsa ne suka aiwsatar da haka. Sannan  idan aka dubi ashabul  Kahfi  suma matasanne,ya ce, wadanda suka rufa ma Manzo baya a lokacin kiransa irinsu Imam Ali ,Sayyida Zahara(AS)  da sauran su  ,za a ga cewa dai matasan ne.ya kara da cewa, haka ma Mujaddadai  irinsu Shehu dan Fodiyu Da Imam Khomenei (KS) duk matasa ne suka dafa masu sai ya ce duk wannan yana nuna maka cewa,matasa sune  jari na duniya da Lahira, kuma akan yarinta ake gina duniya da Lahira,ya kara bayyana cewa, “ba girman jiki bane , zuciya ce mai kyau da ta  siffantu da ibada.” sai  ya ankarar da matasa akan yunkurin da makiya suke yi na  rosa tarbiyyarsusannan ya   nuna wajabcin lura tare  da kauce ma afkawa cikin hadartin wannan tarko. Sai ya bayyana mafita daga wannan tarko da cewa, itace addini ,”a dasa ma matashi tsoron Allah, ibada da son  Lahira tare da tsaron azabarta ,”kuma wannan shi ne manufar kiran Sayyid  Zakzaky(H) ,  ba  al’amarin neman mukamin duniya ba ne”,
Ta bangaren Sayyida Zahara(AS) kuwa, Malam Yakubu ya tabo wasu kadan daga matsayai  da falalolin da Allah ya bata Musamman Tsayuwarta dadagewarta akan bin Allah da taimaka ma sakon da aka aiko Manzo  Da shi,sannan ya bayyana  cewa, al’amarin ahlul Bayt abu ne  mai hatsari domin kuwa abu ne wanda ya shafi Imani.Ya kara da cewa,zaka ga mutum ya yi imani da sakon Manzo a dunkule , amma  da an ce ayi dalla-dalla sai ka ga yana shafa keya bai yarda ba. Ya tabo abubuwa da dama  da suka shafi  hakkkin ahlul Bayt da suka hada da Khumusi,Wila’a  da jagorancin su  kamar maganar  ‘ Halifofi bayana Sha biyu ne” kamar  yadda yake a littafan Buhari da MUsulimu, amma dai mutane  ba su yarda ba, inda zaka ga babban Malami idan aka yi masa wannan bayani baya yarda, haka kuma yake ga sauran musulmin duniya. Sai ya yi mamakin yadda kiriri aka maida Halifofin Annabi  guda Hudu, bayan shi Annabin ya ce Sha biyu ne kamar yadda ya zo a Buhari da Muslim,  ya ce “lallai akwai hadari akan wannan” ya kammala da cewa, ” Ba so bane kawai, a‘a  bi ne ga wadannan  bayin Allah” 




1 comment:

  1. Allah ya kara maimaita mana na wasu shekarun cikin imani da biyayya,

    ReplyDelete