Zama matashi mai addini babban matsayi ne, kuma falala ce daga Allah(T). Malam Yakubu
Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabin mauludin Syyida
Azzahara(AS) da dandalin matasan harkar musulunci karkashin jagorancin Sayyid Zakzaky(H) na yankin da’irar Katsina da kewaye
ya shirya ya kuma gabatar a dakin taro na ‘Shema youth empowerment Centre’ dake garin Kankia, jihar Katsina, a
ranar Lahadi 7 /7/1433.
Malam Yakubu ya ci
gaba da cewa, duniya gaba dayanta, a wannan lokaci matasa ne suke tafiyar da
ita, ina ya bada misali da manyan kasashen duniya dama wannan kasa da cewa,shugabanninsu duk
matasa ne, haka idan aka dubi rundunonin soji
da sauran jami’an tsaro na duniya,
duk za a ga dai matasa ne suke
jagorantar su, ya ce, duk wasu bangarorin tafiyar da al’amurran al’umma dai
zaka ga cewa,matasane ke rike da su. Ya ce, hakama lamarin Lahira ta matasance,inda ya bayyana Imam Hasan da Husaini (AS) a
matsayin shugabannin aljanna. ya kuma karanto kissar Annabawan Allah da suka
hada da Annabi Ibrahim da sauransu da irin gwagwarmayarsu da zalunci duk suna
matsayin matsa ne suka aiwsatar da haka. Sannan idan aka dubi ashabul Kahfi suma
matasanne,ya ce, wadanda suka rufa ma Manzo baya a lokacin kiransa irinsu Imam Ali
,Sayyida Zahara(AS) da sauran su ,za a ga cewa dai matasan ne.ya kara da cewa,
haka ma Mujaddadai irinsu Shehu dan
Fodiyu Da Imam Khomenei (KS) duk matasa ne suka dafa masu sai ya ce duk wannan
yana nuna maka cewa,matasa sune jari na
duniya da Lahira, kuma akan yarinta ake gina duniya da Lahira,ya kara bayyana
cewa, “ba girman jiki bane , zuciya ce mai kyau da ta siffantu da ibada.” sai ya ankarar da matasa akan yunkurin da makiya
suke yi na rosa tarbiyyarsusannan
ya nuna wajabcin lura tare da kauce ma afkawa cikin hadartin wannan
tarko. Sai ya bayyana mafita daga wannan tarko da cewa, itace addini ,”a dasa
ma matashi tsoron Allah, ibada da son Lahira
tare da tsaron azabarta ,”kuma wannan shi ne manufar kiran Sayyid Zakzaky(H) , ba al’amarin
neman mukamin duniya ba ne”,
Ta bangaren Sayyida Zahara(AS) kuwa, Malam Yakubu ya tabo
wasu kadan daga matsayai da falalolin da
Allah ya bata Musamman Tsayuwarta dadagewarta akan bin Allah da taimaka ma
sakon da aka aiko Manzo Da shi,sannan ya
bayyana cewa, al’amarin ahlul Bayt abu ne
mai hatsari domin kuwa abu ne wanda ya
shafi Imani.Ya kara da cewa,zaka ga mutum ya yi imani da sakon Manzo a dunkule ,
amma da an ce ayi dalla-dalla sai ka ga
yana shafa keya bai yarda ba. Ya tabo abubuwa da dama da suka shafi hakkkin ahlul Bayt da suka hada da
Khumusi,Wila’a da jagorancin su kamar maganar
‘ Halifofi bayana Sha biyu ne” kamar yadda yake a littafan Buhari da MUsulimu, amma
dai mutane ba su yarda ba, inda zaka ga
babban Malami idan aka yi masa wannan bayani baya yarda, haka kuma yake ga
sauran musulmin duniya. Sai ya yi mamakin yadda kiriri aka maida Halifofin
Annabi guda Hudu, bayan shi Annabin ya ce
Sha biyu ne kamar yadda ya zo a Buhari da Muslim, ya ce “lallai akwai hadari akan wannan” ya kammala
da cewa, ” Ba so bane kawai, a‘a bi ne
ga wadannan bayin Allah”
Allah ya kara maimaita mana na wasu shekarun cikin imani da biyayya,
ReplyDelete