Sunday, June 10, 2012

ACADAMIC FORUM YANKIN KATSINA YA GABATAR DA TARON MAKON IMAM KHUMEINE(KS) NA WANNAN SHEKARA TA 2012



Aranar Lahadi 10/ 6/ 2012 , dandalin dalibai na Acadamic Forum yankin Katsina ya gabatar da taron tunawa da makon Imam khomene (KS) na wannan shekara a dakin taro na ‘women centre’ dake unguwar  filin samji Katsina.

A jawabin da ya gabatar, Shekh Muhammad Mahmud Turi, wakilin Sayyid  Ibrahim Yakubu Zakzaky(H) a birnin Kano , ya karanto kadan daga tarihin Marigayi Imam Khumene(KS). Malam Turi ya bayyayana cewa, Imam ya  taso ne a gidan Ilimi, amma a yanayi na maraici domin mahaifansa sun rasu tun yana karami,amma a haka ya yi  ta rayuwa irin ta neman ilimi ya kuma rayu a cikin yanayi  karancin abin hannu domin an tabbatar da cewa, a lokacin bargo daya ne kadai ya mallaka, amma a haka ya ci gaba da neman ilimin.Malamin ya  ce, tun yana da kananaan shekaru ya fara koyarwa a Hauza saboda hazaka da Allah (T) ya  ba shi.Malam Turi ya kara bayyana cewa, Allah madaukakin Sarki ya haska ma  Imam halin da al’ummar iran ta ke ciki na rashin bin dokokin Allah, bayan da Imam ya fara wayar ma al’umma da kai sai gwamnatin Sha, ta yi yunkurin kashe shi, abinda ya sa Malamai suka bayyana Imam khomene a matsayin Ayatul lahi, hakan yasa dole Sarki Sha ya janye yunkurin kasha shi, sai dai gwamnatin ta kore shi daga Iran ,inda ya yi hijira zuwa kasar turkiya sannan daga can zuwa kasar iraki, inda a can din ma dai ya ci gaba da wayar ma al’umma kai musamman abin da ya shafi Fikira akan ‘Wilayatul fakihi’ watau jagorancin Malami, wannan kira na imam ya jawo masa kyama daga Malamai.
malam Turi ya kara da cewa, duk lokacin da Musulmi suka yi watsi da tsarin Allah, to rayuwarsu zata kasance a cikin kaskanci, kamar abinda yake faruwa a wannan kasa a halin yanzu. Ya ce, Imam ya ci gaba da kokarin wayar ma mutane kai akan  hadarin bin tsarin gwamnatin da bata musulunci ba domin rashinta gwamnatin musulunci na hana aikatuwar musuluncin. Malam Turi ya kara da cewa, Imam ya yi gwagwarmaya da malamai fiye da yadda ya yi da Kafirai, domoin Malaman suna zarginsa da kawo cikas wajen bayyanar Imam Mahadi(AJ)
Malam Turi ya bayyana wasu darussa da za a dauka a rayuwar wannan bawan Allah inda malamin ya yi tambayar cewa, Mi yasa Imam ya sami wannan nasara , amma ga dimbin Malamai basu sami wannan ba? Sai ya bada amsar cewa, Imam ya na da zuciya daya,sai ya ba Allah(T) wannan zuciya sai Alah ya hore masa zukatan al’umma.  

Malam Turi ya kirayi ‘yanuwa akan yaki da zukata  domin kauce ma abubuwan da za su bata zuciya saboda shagaltar da ita tare da  gurbata ta yadda ba zata iya yunkurin gwagwarmayar  tabbatar da addini ba.
A lokacin da yake kira akan kulawa da tarbiyyar ‘ya’ya, Malam Turi ya bayyana cewa, gurin makiyanmu shi ne  su bata tarbiyyar  musulmi, sai ya bayyana muhimmancin kulawa da  tarbiyyar yara domin su kasance sun sami tarbiyyar addini domin su zamo cikin rundunar da zata zamo ta Allah. Da zata taimakama addini.
A wani bangaren jawabin nasa, ya bayyana cewa, duk jama’ar da tadanfaru da Imam Khomenei, za a ga bambanci da sauran  koda kuwa Shi’a mutum ya ke yi.Ya bada misalin wasu kasahe irin su Pakistan da suke da Shi’a, amma saboda basu damfare da Imam basu sami daukaka ba, amma ga Hizbullahi nan yadda suka buwaya.
A karshe ya bayyana cewa, a wannan kasa babu mafita ga al’umma sai ta hannun Mujaddadin wannan al’umma  Sayyid Zakzaky(H) kamar yadda shehu Usman dan Fodiyo ya  yi bushara.’abinda ya kamace mu shi ne riko da wannan gwagwarmaya ta hanyar kyautata alaka da Allah kamar yadda Sayyid Zakzaky(H) ya ke kira akai’

No comments:

Post a Comment