Monday, November 15, 2010

LAJNAR ISLAMIYYU KARKASHIN HARKAR MUSULUNCI TA GABATAR DA ADDU'AR KWANA ARBA'IN DA RASUWAR MALAM ISHAQ RAFIN DADI

Daga: AbdulAzizi

Lajnar Madarisil Islamiyyah tahti Harakatil Islamiyya ta da'irar Katsina ta shirya tare da gudanar da tunawa da kwana arb'in da rasuwar Malam Ishaq Rafin dadi Katsina da yammacin ranar Talata 3/ 12/ 1431.

Da yake gabatar da takaitaccen jawabi a gaban kabarin Malam Ishaq, Malam Shehu Dalhatu Karkarku wanda ya wakilci Malam Yakubu Yahaya wakilin 'yanuwa almajiran Malam Zakzaky(H) na Katsina, ya fara ne da gabatar da sakon Malam yakubu, inda ya ce,"Malam Yakubu din yana jaddada ta'aziyyarsa ga 'ya'ya , 'yanuwa da almajiran Malam Ishaq gami da mika wannan ta'ziyya ga 'yanuwa almajiran Malam Zakzaky(H) dangane da wannan babban rashi da mukayi" Malam Shehu wanda ya bayyana cewa Malam Yakubu ya yi gurin ya kasance da shi ne ake gabatar da wannan tunawa da rasauwar wannan bawan Allah ,amma saboda kasantuwar ya yi tafiya bai sami damar kasancewa a wannan muhalli ba.

Malam Shehu Ya bayyana cewa Hakika Allah ya karbi rayuwar Malam Ishaq a daidai lokacin da al'umma ke da bukatuwa zuwa ga shiryarwarsa wanda ya dake akan gaskiya duk da tsangwama da yayi ta fuskanta, amma ya dake har Allah ya tabbatar da dugadugansa kamar yadda muka gani. Malam Shehu ya ce, ba shi kadai yake kwance a wannan wuri ba,amma ga shi Allah ya taro masa zukatan Muminai masu kuka dangane da rasa shi, suka baro wuraren ayyukansu suka kawo masa wannan ziyara ta kwana arba'in domin tunawa duk dai albarkacin kiran da Malam din yake yi duk dawannan tsangwama da ya hadu da ita domin raya al'amarin Addini.Sai ya bayyna wannan rasuwa ta Malam Ishaq da cewa, :tunatarwa ce, "ya rage ga remu da muka saura " sai ya yi kira ga 'yanuwa da su yi shiri domin fuskantar wannan rana ta mutuwa.

Malam Shehu ya kuma yi kira ga Malamai na wannan gari, da su yi koyi da Marigayi Malam Ishaq ta hanyar hada kan almajiransa da sauran Musulmi ba kokarin raba kan su ba.

Malam Abubakar Kofar Durbi wanda ya wakilci Shugaban Lajnar Malam yakubu Idris , ya bayyana cewa makasudin shirya wannan tunawa da rasuwar Malam Ishaq, shine domin tabbatar da zumuncin dake tsakanin Malam da 'yuanuwa. ya bayyana cewa shirya wannan munasaba, an yi ta ne bisa umurnin Malam Yakubu Yahaya wanda ya karfafa akan gabatar da ita domin a hadu a bayyana ayyukan wannan bawan Allah . Ya kara da cewa, an gayyato 'yanuwa 'ya'ya da almajiran Malam Ishaq ne ga mi da shirya wasu addu'o'i da karatun al'Qur'ani mai tsarki tare da gabatar da jawabai da babban dansa da kuma almajirinsa hada da Wakilin Malam Yakubu Yahaya zasu gabatar da daren na wannan rana ta Talata domin a bayyana ma jama'a irin gudun muwar da yake bayarwa wajen amsa kiran hadin kan musulmi da Malam Zakaky(H ) yake jagoranta a wannan nahiya., musamman ganin shi kadai ne wanda ya yi fice wajen karba kiran hadin kai da ake yi duk lokacin Mauludin Annabi(SAW) a duk shekara.

A Jawaban da aka gabatar da dare, Manyan almajiran Marigayi Malam Ishaq suka gabatar da jawabai a takaice kan yanda Malam din ya yi kokarin ganin ya koyar da su al'amurra na addini da dama, ciki kuwa har da nuna kauna ga Manzon Allah wanda dama shine abinda Malam Ishaq ya yi fice aka kuma sanshi akan haka.

Malam Ishaq ya yi fice wajen karba kiran makon hadin kai da harkar musulunci ki gabatarwa a duk shekara, shine Malami kwara daya da baya tsoron nuna goyon bayansa ga kiran Malam Duk da cecekucen da yake gamnuwa da shi a tsakanin Malaman garin Katsina akan yadda yake gwamatsar almajiran Malam Zakzaky(H). Taron kareshe da ya halarta na makon hadin kai da Da'irar Katsina ta shirya a mauludin da ya gabata , ya nuna a wajen cewa, babu wani abin da zaya hana shi halartar taron nuna mauludin Manzon Allah, gami da sauran jawabai da ya yi masu matukar gamsarwa da sallamawa ga kiran Malam(H).

Malam Ishaq ya rasu a yanayin da duk wani mumini yake fatan ya yi irin wannan rasuwa, ya rasu a daren Juma'a kuma yana kalmar shahada tare da girmama Allha madaukakin sarki.

Al'ummar da suka hadu wajen wannan zikira duk sun kasance cikin wani yanayi na damuwa da juyayin tunawa da wannan bawan Allah. An yi addu'o'in fatan Allah ta'ala ya tabbatar da kyakkyawan fatan da Muminai suke yi akan sa, da fatan kara gabatar masa da karin adduar nema kasancewa tare da Manzon Allah(SAW) wanda Malamin ya yi suna waje gaba da duk wanda ya kuskura ya yi sakin baki a kan Mauludin haifuwarsa.


Thursday, October 28, 2010

AN GABATAR DA WA'AZIN GORON SALLAH A ZANGON ALARAMMA


Daga: Abdul'Hamid Sani Ilya

Ranar Asabar 9 ga Shawwal, 1431 da yamma `yan uwa Musulmi almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na garin Zangon Alaramma da ke kusa da garin Tsakatsa a Charanci jihar Katsina suka gabatar da Wa’azin goron Salla a garin Zango.
Wanda ya gabatar da Wa’azin a garin ga dimbin al’ummar Musulmin da suka taru don sauraren, shine Wakilin ‘Yanuwa almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na yankin Ganuwa, Rawayau da Kewaye,watau Malam Abdulhamid Iliya Ganuwa.
Malamin ya yi kira ga al’ummar Musulmi da cewa, “Lalle ya kamata mu tuna da makasudin abin da ya sa Allah Ya halicce mu, kuma Ya kawo mu wannan Duniyar da muke rayuwa a cikinta, wadda ko ba-dade ko ba-jima zuwa gare shi zamu koma ko mun so ko mun ki”.
Ya kara da cewa, “A she, in kuwa haka ne, ya zama wajibi a gare mu, musamman mu Musulmi, musan yadda zamu bautawa Allah Madaukkin Sarki ta hanyar bin dokokinsa wadanda ya aiko Manzonsa, Annabi Muhammadu (S) da su zuwa ga bayinsa don mu samu tsira  da kyakkyawan sakamako a wurin Allah ya yin da muka koma zuwa gare Shi a gobe Lahira.”
Sannan Malam Abdulhamid ya karanto ayar nan ta cikin AlKur’ani mai girma wadda Allah Ta’alah ke cewa, “Kuma ban halitta Aljannu da Mutane ba sai domin su bauta mani.” Sai Malam Abdulhamid ya ce, “Hakika wannan ayar ta na nuna mana makasudin abin da ya sa Allah Ta’alah Ya halicci Aljannu da Mutane.”
Kuma ya ci gaba da cewa, “Don haka ba wanda ya cancanci a bautamawa in ba Allah Madaukakin Sarki ba! Kuma wannan shine abin da Allah Ya ke ummurtarmu da shi  a waccan ayar ta Alkur’ani mai girma.
Malam Abdulhamid ya ci gaba da cewa, “In ko muna san musan yadda Allah Ta’alah Ke son a bauta masa, ya zama ba makawa gare mu dole sai mun komawa bin dokokin Allah Ta’alah kai tsaye in har muna son mu fassara waccan ayar da aikata ta a aikace yadda Allah (SWT) Ke so.”
Ya kara da cewa, “ Saboda haka wajibin mu ne mu bi koyarwar Manzon Allah, Annabi Muhammadu (S) da kuma koyarwar Iyalan gidansa tsarkaka, ma’asumai in har muna son musan yadda Allah Ta’alah ke son a bauta masa don mu samu tsira a Lahira! “Wannan kuma shine kiran da Maulana, Mujaddadi, Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya kwashe sama da shekara talatin ya na yi wa bayin Allah da ke wannan nahiya bayani domin mu koma wa bin tsarin dokokin Allah (SWT) in har mu na son mu samu tsira daga azaba a gobe lahira.”

Malam Abdulhamid ya ce, “Godiya da yabo sun tabbata ga Allah Madaukkian Sarki da Ya fahimtar da mu wannan kiran na a komawa tsarin Allah da dokokinsa da Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ke yi a halin da ake ciki yanzu. Tare da fatar Allah Ya amfanar da mu abin da muka ji, Ya kuma ba mu ikon aikatawa.”    

Saturday, September 18, 2010

HOTUNAN BIKIN TAYA FUDIYYAH RIJIYAR LEMU MURNAR HARDACE AL'QUR'QNI DA DALIBANTA SUKA YI

WASU DAGA HOTUNAN DA MUKA SAMU NA BIKIN TAYA FUDIYYAH RIJIYAR LEMU MURNAR HARDAR AL'QUR'ANI DA DALIBANTA NA BANGAREN TAHFIZ SUKA YI.
MUN SAMU HOTUNAN DAGA:   HARKARMUSULUNCI.ORG

 
Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron


 wasu daga cikin Dalibai suna gabatar da Pared a lokacin gabatar da bikin


wasu da suka hardace Al'Qur'anin suna gabatar da karatu a gaban Alaramma Gwani Lawi
Wani sashe na 'yanuwa suna sauraren jawabin Sayyid Zakzaky(H) a wajen taron

TARON TAYA FUDIYYAH RIJIYAR LEMU KANO MURNAR BIKIN HARDACE AL'QUR'ANI MAI GIRMA DA DALIBANTA NA BANGAREN TAHFIZ SUKA YI.

Daga:AbdulHamid Ilya Ganuwa,
08162234919 / 08125661551
Taro, ya yi taro! Ba shakka taron da Makarantar Fudiyya Rijiyar Lemu ta kira a

garin Kano, a madadin Da’irar Kano don bikin taya murna ga daliban da Allah Ya horewa haddace littafi mai girma,watau Alkur’ani mai tsarki, wadda aka gabatar a garin Kano, ranar Lahadi 4 ga watan Shawwal ya yi nasara.

Babbar nasarar da taron ya samu, itace halartar babban Bako, Shehu, Mujaddadi, Sayyid Malam Ibraheem Ya’aqub Zakzaky (H) wanda ya shafe sama da shekaru talatin yana kiran al’ummar Musulmin kasar nan da a koma wa bin tsarin Allah Ta’alah, watau bin dokokin Allah da ke cikin Alkur’ani mai girma.

Wannan gagarumin taro da aka gabatar a bi sa jagoranci da kuma kulawar mai masaukin baki, Wakilin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) a birnin Kano, Malam Muhammad Mahmud Turi, ya samu halartar Sayyid Malam Ibraheem Zakzaky (H) tare da Amirorin `yan uwa na garuruwa da kauyuka da ke sassan kasar nan.

Haka ma taron ya samu halartar manyan bakin da aka gayyata a cikin birnin Kano da wasu sauran garuruwa a wannan kasa. Kadan daga cikin bakin da suka samu halartar taron sun hada da, Shugaban Mahaddata Alkur’ani mai girma na Kano, Shugaban Shariffai na Kano, Alarammomi Mahaddata kuma Marubuta Alkur’ani mai girma, Limaman Masallatan Juma’a da sauran dimbin bakin da ban iya kiyaye sunayensu ba.

Dubban `yan uwa Musulmi almajiran Sayyid, Malam Ibraheem Zakzaky (H) na cikin birnin Kano da sauran garuruwa da kauyukan Kasar nan maza da mata, manya, yara da tsofaffi da `yan uwa na Jamhuriyyar Kasar Nijar sun samu halartar wannan taro na taya daliban Fudiyya Rijiyar Lemu murnar samun nasarar hardace Alkur’ani mai girma.

Wannan taron taya yara murnar haddace Alkur’ani mai girma ya samu gagarumar hidima ta kai-kawo, shirye-shiye da tsare-tsare da abin da ka-je-ya-dawo a bisa kulawar dakarun Harka Islamiyya, watau Hurras.

Suma `yan ISMA, watau masu kula da lafiyar al’umma a Harka Islamiyya, sun bayar da tasu gudumuwar sosai a wajen kulawa da marasa lafiya a yayin gudanar da taron.

Haka suma Sha’irai, watau Mawaka Harka Islamiyya sun jiyar tare da dadadawa mahalarta wannan gagarumin taro baitocin wakoki masu dadin gaske kafin fara taron da kuma bayan gama jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

Masu aikawa kafafen watsa labaru da rahotonni, da aka fi sani da `yan Jarida da masu daukar hotuna, suma sun samu halartar wannan kasaitaccen biki na taya yara murnar haddace Alkur’ani mai girma da aka yi a birnin na Kano.

A filin taron dai an samu tsara rumfuna kamar haka, Rumfar Babban Bako Sayyid Malam Ibraheem Zakzaky (H). A kwai kuma Rumfar Manyan Baki da aka gayyata.

A kwai kuma Rumfar `yan uwa mata, watau sisters, Rumfar Sharifai, Rumafar Alarammomi, Rumfar Limaman Juma’a, Rumfar `yan Jarida, Rumfar `yan ISMA, Rumfar almajiran Sayyid Zakzaky (H) da suka fito daga wasu garuruwan kasar nan da Kauyuka da kuma Rumfar yara maza da mata Mahardata Alkur’ani mai girma da dai sauran rumfuna masu yawa.

A can bayan filin taron kuwa `yan tijara (`yan kasuwa) ne suka baje kayayyakin sayarwa iri-iri, kala daban-daban don masu bukata. A waje daya kuma masu sayar da abinci ne da masu sayar da ruwa ga wadanda Allah Ya ba ikon halartar wannan taro da aka yi a wannan rana ta lahadi.

Kadan daga cikin manyan matsalolin da na lura da afkuwarsu a wannan taro mai muhimmancin gaske sune, rashin isar masu tsara wajen taron da wuri, wanda hakan ya kawo kurewar lokaci a yayin taron, musamman takaitaccen lokacin da Sayyid ya amfana da shi ya yin ya gabatar da jawabi.

Sai kuma matsalar kayan sauti, musamman lokacin da ake gabatar da yaran da aka shirya taron don taya su murnar haddace Alku’ani mai girma sadda ake gabatar da su ga mahalarta taron a ya yin da suke karanta Ayoyin Alkur’ani mai girma, wanda ba’a samu jin karatun na su a wurin taron sosai ba.

Sannan kuma rashin jin sautin ya jawo daruruwan mahalarta taron da ke can baya wadanda muka samu zantawa da su, sun shaida mana cewa ba su ji jawabin da Sayyid Zakzaky (H) ya yi ba, kasancewar sauti bai kai wa in da suke. Da fatan Allah Ya bamu ikon gyarawa.

Saturday, September 11, 2010

AN GABATAR DA WA'AZIN GORON SALLAH KARAMA (IDIL-FITR) NA WANNAN SHEKARA TA 1423 A KATSINA

DAGA: ABDUL'AZIZI

Da Yammacin ranar Juma'a ne 02/10/1431 ,Da'irar'yanuwa Musulmi almajiran Sayyid Ibarahim Zakzaky(H) ta Katsina da kewaye ta shirya tare da gabatar da wa'azin goron Sallah a babban masallacin Juma'a na cikin garin Katsina,a karkashin jagorancin Malam Yakubu Yahaya .


A jawabin da ya gabatar Malam Yakubu ya bayyana cewa,
“Shugabanni ke fada da mu, ba mu ke fada da shugabanni ba"
Malam Yakubu ya ci gaba da cewa abinda muka sani Mu bayin Allah ne, kuma mun san cewa Allah ya raba shugabanni zuwa gida biyu, masu shiryatarwa da umurnin Allah horo da kyakkyawa da hani ga mummuna da kuma masu kira zuwa ga shedan. Kuma wannan shine abinda Allah ya tsara” Ya ce kuma wannan shine abinda Sayyid Zakzaky(H) ya kwashe sama da shekaru 30 ya na kira zuwa ga reshi cewa, ba za a bi shugabancin masu kira zuwa ga bata ba " Mu ba fada muke da shugabanni ba su ma ne ke yin fada da mu” domin ba mu yarda da bin shugabani masu kira zuwa ga bata ba, wannan shine ma matsalar idan ma akwai matsala, domin suma shugabannin dole ne akansu su bi Allah (T). sai ya kara da cewa, lokacin boye-boye akan bayyana addini ya wuce idan dai har mabarnata za su dinga shelanta wannan barna tasu a kafofin yada labarai a Duniya, to kamata yayi musulmi su yayata addininsu. Malam Yakubu Ya nuna takaicin jin yadda Malamai a wannan wata na Azumi suka yi ta yayata ayi addu'a ga wadanna shuwagabanni masu jagorantar mutane bada littafin Allah ba. Ya ci gaba da bayyana cewa, wasu suna cewa ai wannan kasace mai addinai kamar kuma yadda yake a tsarin mulkinta, amma kuma Allah shi cewa ya yi, "addini a wurinsa shine musulunci" sai ya yi tambayar cewa, yaya zaka yi ka gamsar da Allah(T) idan kace ka yarda da cewa kasa ce mai addinai ga shi kuma Allah ya ce "wanda duk ya riki wani addini ba musulunci ba, ba a karba masa ba kuma a Lahira yana cikin tababbu'.Tunda Allah ya ce haka, to kai kuma tsammaninka Allah ya yarda da tsarin da ake tafiya akansa da jagorancin da ake da shi a wannan kasa?

Malam Yakubu ya ci gaba da bayyana cewa, wasu suna ganin addini a matsayin ci baya wanda kuma aka ga yana rike da addinin ana ganinsa cibayayye, a ganin masu wannan ra'ayi, rayuwar Turawa ita ce cigaba da kuma wayewa.Sai ya kawo misalin irin wadannan kasashe da ake ganin sun ci gaba da cewa, a halin yanzu saboda tabarbarewr atarbiyya, gami da aikata munanan laifuka har dokar ta baci ake sawa a wasu kasashen domin maganin aikata muggan laifuka. Sai ya ce, addini ne kadai zai yi maganin irin wadannan matsaloli.

Da ya tabo irin yadda al'umma ke kauce ma wahalhalu akan kin bin tafarkin addini ,sai ya ce, Allah ya halicci mutum ne a cikin wahala ba domin jin dadi ba a wannan duniya' Allah ne kuma ya tsara ma dan Adam irin wahalar da za ya sha daga cikin wahalar kuma har da akwai jihadi da Ibada wadda cikinta har da Azumi wanda aka kammala, shi ma yana daga cikin irin wannan wahala, yace kuma shi wannan Azumi Allah ya sanya daga cikin hikimominsa har da gyara halayen mutum, domin shi mutum yana da wasu halaye munana kamar fushi, sha'awa da sauransu wadanda idan mutum yana yin Azumin, to za ya daidata masa wadanna halaye ta hanyar tsoron Allah da zaya samu. Sai ya nuna wajabcin yin addini domin shine za ya gyara dan Adam.Malam Yakubu ya kawo irin yadda Annabawan Allah suka yi tsayin daka wajen fuskantar wadannan wahalhalu haka ma Mujaddadai domin dai kawai a tseratar da dan Adam daga shiga azaba a Lahira, sai ya yi kira ga Malamai da su fada ma jama'a gaskiya.




A tun farko sai da Malam Yakubu ya bayyana yadda wannan wa'azi na goron Sallah ya samo a sali a wajen 'yanuwa a wannan gari, inda ya ce , tun farko lokacin 'yanuwa ba su da yawa ,idan irin wannan lokaci ya zo , akan kai ma juna ziyara ne saboda neman ladar dake akwai ga yin ziyarar, daga baya da aka kara yawaita ya zamo ba za a iya zuwa gidajen junaba , sai aka fara gabatar da shi a wannan muhalli, ganin kuma yadda jama'a ke lekowa sai aka rika nasihantar Juna domin samun amfanuwa.

A karshe ya yi fatan Allah ya kawo ma wannan al'umma mafita daga wannan mawuyacin hali da ake ciki.


 Malam Yakubu Yahaya Katsina a lokacin da aka gabatar da goron Sallah
  

Friday, September 3, 2010

AN GUDANAR DA MUZAHARAR KUDUS A KATSINA

Daga Abdul Aziz

A ranar Juma’a 25/09/1431 wanda ya zo daidai da 3/09/2010 aka gudanar da muzaharar nuna goyon baya ga al’ummar Palastinawa da haramtaciyar Kasar Yahudawan Sahayoniyya ta Isra’ila suka kwashe shekaru kimanin sittin da uku ( 63) suna zalunta ta hanyar kisa , kamawa, rusa gidaje gami da killacewa.

Muzaharar wadda aka fara ta bayan kamala Sallar Juma’a, ta bi manyan titunan cikin garin Katsina da ta soma daga titin Mobil ta bi ta sabon layi, ta fice ta unguwar Kerau, sannan ta fito babban Asibitin Katsina ta dawo inda aka kammalata a bakin shatale-talen da ke bakin Masallacin Juma’a na cikin garin na Katsina.

Muzaharar wadda dandazon ‘Yanuwa Mazansu da Matansu suka fito daga sassa daban-daban na Da’irar ta Katsina da kewaye suna rera wakokin da ke bayar da sakon nuna goyon baya ga wadannan raunana da aka kwashe wadancan shekaru ana zalunta ta hanyoyi da dama.

A jawabin da ya gabatar bayan kamala wannan muzahara, Malam Yakubu Yahaya wanda akarkashin jagonacin sa aka gudanar da wannan muzahara, ya bayyana cewa,wajibi ne da ya hau kan dukkan al’ummar Musulmi su aiwatar da iri wannan jerin gwano domin kuwa duk lokacin da al’ummar Musulmi ta shiga wani hali, to wajibin sauran al’umma ne su nuna goyon bayansu. Sai ya yi nuni da cewa, irin wannan muzahara ana gudanar da ita ne a duk fadin Duniya baki daya domin nuna goyon baya ga al’ummar Palastinu da aka share shekaru sittin da uku ana gallaza masu.

A wani bangare na jawabin Malam Yakubu ya dan tabo tarihin yadda aka kwaso Yahudawa aka jibge su a wannan wuri na Palastinawa, abin da ya bayyana da cewa dama kutungwila ce aka shirya. Ya yi nuni da yadda Yahudawan suke ‘yan tsiraru, amma sun addabi al’umma saboda yadda suka goge da munafunci da kulle-kulle sai yace, “ babu abinda ke maganin Yahudu illa addini” ya ce siyasa, yarjejeniya da Majalisar Dinkin Duniya duk basu maganin Yahudu, saboda su mutane ne da suke bukatar zubar da jini musamman ma na Musulmi. Ya kara da cewa, duk wata yarjejeniya da za a shirya da su sai sun warware ta kamar yadda Allah ( T ) ya bayyana a cikin al’Qur’ani da cewa, “suna warware alkawali duk sa’adda aka yi shi” Sai ya yi nuni da cewa, duk wani zaman taro ko yarjejeniyar sulhu duk ana yinsa ne a ISKA. Sai ya ce maganin wannan shine “idan Yahudu suna da akidar mamaya da zubar da jinni; to su kuma Musulmi suna da akidar shahada da shiga Aljanna” wannan kuma shine maganin Yahudu sannan kuma wannan abu ne mai yiwuwa domin an gwada a baya a lokacin da ‘yan Ikhwanu na Misra suka fafata da yahudawa abin da ya sa aka kulla makircin kama Mujahidai, ya ce, amma a yanzu Allah ya sake ta do wasu mujahidan irinsu Hizbullahi da Hamas ga kuma Jamhuriyar Musulunci ta Iran, wadanda kullum a shirye suke su yi maganin Yahudawan.

Sannan ya yi nuni da cewa, irin wannan muzahara da ake yi tana da tasiri, domin yanzu suna ganin duk duniya tana kware masu baya ne. sai ya yi kira da cewa kada mutum ya ga irin wannan tarurruka da ake yi wani abu ne na sha’awa ko marmari, a’a yana da makasudi kuma Allah yana isar da wannan makasudi. Saboda ana yi ne domin Allah da kuma amsa kiran Manzon Allah da ya ce,” wanda ya ji wani Musulmi yana neman taimako amma bai taimake shi ba , to shi ba Musulmi ba ne”sai ya ce wannan yana daga cikin irin gudunmuwar da muke iya bayarwa. Ya yi fatan Allah ya nuna mana kaskantar wadannan Yahudawa.

KUDUS DAY PICTURES BY MOHAMMED ZAHARADEEN KATSINA