Tuesday, May 15, 2012

MUZAHARAR MAULUDIN SAYYIDA FATIMA AZZAHARA (AS) A KATSINA




‘yayanuwa mata almajiran Sayyid Ibarahim Zakzaky(H) dake  da’irar  Katsina, sun shirya  tare da gabatar da  muzaharar  mauludin Sayyida  Fatima azzhara diyar Manzon Allah (S) ta wannan shekara a wannan rana ta Talata,24/6/  1433 
.
Muzaharar  wadda  aka soma da misalin karfe tara da rabi na safiyar  wannan  rana , ta sami halartar ‘yanuwa  mata  daga yankuna  daban-daban na cikin garin Katsina  da kewaye, a  bisa      rakiyar Harisawa  da  suke a goshin wannan muzahara , sannan ‘yan makarantun Islamiyyu na ciki da wajen garin  Katsina da suke dauke da tutoci iri daban-daban  ana tafe mawakan Harkar musulunci na rero baitocin  yabo ga Sayyida Fatima(AS)  dama wakokin mahaifin ta da sauran “ya’yanta  A’immatul huda(AS).
Muzaharar  wadda  ta zagaye  muhimman  titunan garin Katsina, ta kayatar ainun ida aka kwatanta ta da wadanda suka gabace ta, duk da karacin abubuwa kamar yadda daya daga cikin masu shirya ta  ta shaida ma  manema  labarai da suka zanta da ita. Malam Bilkisu idris  ta ce, “akwai shirye-shirye da  za a gabatar idan Allah ya nuna mana ta shekara mai zuwa, wanda ta ce, za su fadada shirin domin gayyato mata daga bangarori da yawa na cikin garin Katsina.
A jawabin da ta gabatar bayan kammala wannan muzahar, Malama Safiya Kabir, ta bayyana  wasu kadan daga cikin matsayai  na wannan  baiwar Allah da cewa, ita  ce wadda Allah da kansa ya daura mata aure da babban bawansa Imam Ali (AS), sannan ta bayyana takaicin irin wahalhalu da wannan baiwar Allah ta hadu da su tun bayan wafatin mahaifinta  Annabi  Muhammad (S).Ta ce, a yunkurin rufe matsayi  da darajarta  ne,  ba za ka taba jin ana karanto wasu Hadisai da za a danganta ruwayarsu daga wajen ta ba, domin  kada jama’a  su fahinci wasicin da Annabi ya yi  na bain  shiriya a hannun jikokinta, sai tayi  fatan al’umma  musamman ‘yanuwa  mata  za su yi bita akan rayuwarta su kuma yi koyi da halaye irin na Fadima(AS).
Kafin wannan muzahar, sai da kwamitin ‘yanuwan mata ya gabatar da wata ziyara zuwa ga malaman makarantun  allo dake yankuna  hudu na bangarorin da ake da su  a wannan  da’ira  da suka hada da yankunan  Gabas, Yamma, Kudu da kuma Arewa  wtau  (Zones) tare da gabatar ma almajirai da malamansu  kyaututtuka  na  abinci  da kuma sabulan wanki albarkacin wannan baiwar Allah .
Za dai aci gaba da gabatr da wannan gagarumin biki na tuna haifuwar diyar Manzon Allah Fatima azzhara (AS)  a rana daya da ta rage  inda Malam Yakubu Yahaya zaya gabatar da jawabin karshe na wannan biki.


Sunday, May 6, 2012

A KARO NA UKU: AN TUNA DA SHAHADAR ALHAJI IBRAHIM HAMDALA CHARANCI


A karo na uku, Mu’assasatus shuhada  da   bangaren ‘yanuwa na kwamitin ahl-duthour  yankin da’irar Katsina, suka gabatar da taron tunawa da shahadar  Alhaji Ibrahim  hamdala  Charanci  dake  jihar  Katsina  da yammacin ranar Assabat 14/6/1433.
 A jawabin da ya gabatar, Malam  Shehu  Dalhatu  Karkarku, ya bayyana Shahada  da cewa falala  ce da Allah (T) yake  bayar da ita ga daidaikun bayinsa musamman a irin wannan lokaci da al’umma bata  bisa tsarin  Allah. Malam Shehu Dalhatu ya bayyana matakai  da Shehu Usmanu  Mujaddadi  ya  bayyana da suka wajaba musulmi su dauka  a duk lokacin  da suka  sami  kansu a wurin da ba  a bin dokokin Allah, wadannan  abubuwa  kuwa  sune, kauracewa  daga wannan wuri  da ya  bijire  ma tsarin  Allah, ko kuma gwagwarmayar  tabbatar  da tsarin  Allah din  ko  kuma mutum  ya tafi daji ya sami wata itaciya ya ciza har sai ya mutu.
Ya yi tir da  yadda  ake  ta yunkurin  bata  kiran komawa  ga tsarin Allah  da sukar kiran da sunan ana shi’a, wai kuma shi’ar  ba addini ba ne. Yace, “amma kiran shi ne mafita ga al’umma  daga wannan yanayi  na zalunci da ake ciki” daga nan Malam Shehu ya gutsuro matsayin shahidi da bayyana kadan daga  cikin matsayan da suka hada da , ceton mutane  saba’in  daga cikin danginsa,  bayan  rahama da yake  cikinta  tun kafin tashin kiyama. Ga makasan Alhaji Ibrahim kuwa,  ya bayyana matsayinsu ne na dawwama cikin azabar wuta  kamar yadda Allah(T) ya fada a cikin littafinsa mai tsarki.
A tun farko sai da aka gabatar da ziyarar Shahidin a makwancinsa, inda Malam Muhammad Awwal  Iyal Zariya  ya gabatar da takaitaccen jawabin da a cikinsa ya tunatar akan irin ta’addancin da aka yi ma Alhaji Ibrahim  na kisan gilla ba domin komi ba  sai dai saboda imaninsa. Ya  kawo misalin halin da al’umma take  ciki na zalunci da kashe-kashe  da ake ta yi  akan musulmi, inda ya bayyana mafita daga wannan yanayi  sa cewa, ita ce, matsayar da Imamu Husaini(AS) ya dauka a lokacin da ya ga addinin Manzon Allah  yana fuskantar  rusawa, abinda ya kai ga shahadarsa .malam Awwal ya kara da cewa, gwagwarmaya a irin wannan lokaci ita ce kawai mafita, ya yi nuni da cewa, ko a kasashe irin su Iraki da  Amerika  ta kai mamaya  tana kashe  jama’ar  kasar, g wagwarmaya  suka yi  har sai da Amurka din ta ga babu wurin zama sannan ta fara janye sojojinta  daga kasar. Sai ya ce a wannan  kasar ma gwagwarmaya  karkashin jagorancin  Sayyid Zakzaky(H) tare  da  tsayuwa  akan tafarki  ne  kadai zaya kawo  mafita ma wannan al’umma .
Idan za a iya tunawa, kimanin shekaru uku  da suka gabata ne,  wasu  gungun ‘yan ta’adda  suka kai ma shahid  Alhaji  Ibarahim Hamdala hari a gidansa bayan ya tashi daga shagonsa, inda suka sassare shi har suka shahadantar da shi.
‘Yanuwa daga garuruwa da dama  ne suka sami halartar wannan tunawa  da shahadar  tasa.  




Sunday, April 22, 2012

MU'ASSASATUS SHUAHADA'U TA GABATAR DA TARON KARA MA JUNA SANI NA WUNI UKU A KATSINA







A karo na biyar, Mu’assasatus Shuhada’u a Harkar musulunci a  Najeriya  da Sayyid Ibrahim Zazaky(H)     yake yi ma jagoranci, ta shirya taron karama juna sani  na ‘ya’yan Shahidan Harkar wanda yankin Shahid Hamza da ke KAtsina  ya shirya  a  garin  tun daga ranar Juma’a  29/5/ ha r  zuwa 1/6/ 1433.
A jawaban da  aka gabatar da suka kunshi muhadarori da masu jawabai . Dokta Abdullahi  Dan Ladi wanda ya yi jawabi aklan ‘ Ilimi ginshikin rayuwa” ya  bayyana  ilimin  da cewa, haske ne da Allah yake jefa shi a cikin zuciyar wanda ya ga dama, inda  ya  bayyana cewa, kowace halitta da Allah ya samar, to tana da nata ilimi da aka kimsa mata sai dai ilimin yakan bambanta  da na  juna. Dokta Abdullahi  ya bayar da misalai akan halittu na dabbobi da yadda suke rayuwa a tsakaninsu  abisa  ilimi  da Allah  ya hore masu, sai  ya  ce  amma ilimi dan  Adam ya bambanta dana dabba.
Dangane da ilimin Dan Adam,  cewa  ya yi,akwai wanda  mutum  ya  gada  kuma  yake koyo acikin al’uimmar da yake rayuwa  a cikinta sannan wanda ake koyowa a hannun malamai.
Dokta  ya  bayyana cewa, rayuwar mutum bata takaita anan duniya ba, akwai wata rayuwar ta bayan mutuwa, sai  ya ce, duk  wanda aka halitta , to za a yi masa Hisabi, kuma  ana  yi ma mutum  Hisabinne gwargwadon Iliminsa , ya bayyana  cewa, sai mutum  ya san Mahaliccinsa  sannan ne zaya iya bauta masa yadda ya kamata, sannan dole aikin mutum ya tafi kafada da kafada da iliminsa. Sai ya bayyana ilimin boko da cewa da shi da na addini duk daya ne matukar dai mutum ya yi  ilimin  domin Allah  da kuma niyyar taimakama al’umma. Ya kara da cewa, kamar yadda za a iya yi ma mutum azaba akan ilimin boko, to haka ma za a iya yin azabar ga mai ilimin addini madamar mai na  addini  bai yi amfani da ilimin  ba. Sai ya bayyana al’amarin karatu da cewa, ba abune mai sauki ba sai an dage sannan ne ake samunsa. Sai ya bukaci ‘ya’yan Shahidan da su  dage su kokarta su taka duk wani fage na ilimi da ake da shi, kuma a shirye Mu’assasar  take ta dauki  nauyin duk dan Shahidin da ya sami damar kara karatu kowane iri ne .
A jawabin da ya gabatar  Malam Abdull Hamid Bello Shugaban wannan Mu’assasa ta Shahidan Harkar musulunci, ya yi Magana ne akan kyawawan dabi’u, inda ya karanto Hadisai masu dama da suke Magana akan matsayin dabvi’u masu kyawu. Malam Abdul Hamid ya bayyana  tarbiyya   da cewa, ita ce,yin aiki mai kyau da barin maras kyau” Sannan ya bayyana cewa, Allah ya aiko mana da abin koyi watau Manzon Allah (S) wanda yake rahama a cikin halittu,sannan wannan Manzo shine madubi  da zamu kalla domin koyon dabi’u  daga wajen sa.Sai ya bukaci mahalarta da su siffantu da duk dabi’u  kyawawa  na  addini kamar ,gaskiya ,hakuri, yakini akan abinda mutum yake yi ,kyauta da dabi’ar mutunta kai”muru’a”ya kuma bukaci mahalarta su yi dubi cikin lamurransu domin siffantuwa da irin wadannan dabi’u saboda da irinsu ne kawai za a iya kawo gyara a cikin al’umma..
A jawabin kammal  wannan taro da ya  gabatar,  Malam Yakubu Yahaya  ya fara ne da gode ma Allah (T) da ya hukumta yin wannan taro na ‘ya’yan Shahidai masu albarka  a wannan Gari na Katsina,sai ya bayyana Shahada da cewa, ita ce sirrin nasara ”bama addini ba har lamurran rayuwa  ana bukatar sadaukarwa inada ya nusar  ta hanyar kawo wasu misalan al’ummu da suka sadaukar domin  su kubutar da kansu daga danniyar ‘yan mulkin mallaka inda  ya bayar da misalin gwagwarmayar mutanen Kenya da Aljeriya  a yayin kwatar kansu daga Turawa,sannan ya ce. Gwargwadon  sadaukarwarmu, daidai nasara da zamu samu sai ya nuna muhimmancin mu kara sadaukarwa  akan wannan tafarki na Addini” yadda  tarbiyya ta gurbata a wannan al’umma tamu, mafita daga wannan yanayi yana bukatar sadaukarwa”. Malam Yakubu  ya ce, Allah ya yi mana baiwar kasha  99 bisa dari domin ya albarkace  mu da  jagoranci , kuma wannan jagoranci  shi ne  makami na nasar saura kashi  daya  ake bukatar mu aikata, wannan  kashi guda kuma  shi ne “ji da  bi” ga wannan jagora . Malam Yakubun ya jawo hankalin ‘ya’yan Shahidan  da  cewa, su tsayu akan abinda  iyayensu suka sadaukar da rayuwarsun akansa watau gwagwarmayar addini sannan su guji aikata duk abinda za ya bakanta ran mahaifansu domin suna kawo masu ziyara lokaci-lokaci kamar yadda ya tabbata a Hadisin Annabi(S) Ya kuma bukaci  masu kula da iyalan shahidan  da s kara u kula da abubuwan da  yaran  su kanyi , a kwabe su idan suka yi abin da bai kamata ba. Ya tsoratar da yaran cewa, su guji yi kahon cewa, su ‘ya’yan sahidai ne  amma  su basu yin aikin da iyayen nasu suka  yi,  inda  ya  ce wannan ba zaya  fitar da su ba a lahira  sai dai idan sun yi aiki na kwarai . ya  kuma ankarar akan al’amarin wayoyin yaran da cewa, akwai  bukatar a rika kulawa da halin da wayoyin yaran suke ciki, domin akwai makircin bata  tarbiyyar ‘ya’yanmu da aka bollo da shi ta hanyar wayoyin tafi da gidanka.
A wannan mu’tamar an  samu nasarar kai ziyarori a wuraren  tarihi  da suka hada da Hasumiyar Gobarau,da Makabartar Dan Marna  wani waliyyi da aka yi  a Katsina  sai zuwa rijiyar  Gusugu dake birnin Daura tare da ziyatar shahid Ibrahim Muhammad Zariya da ya sami shahadarsa a lokacin waki’ar  janar Abacha.
Manufar shirya wannan taro dai  kamar yadda  Malam Abdul Hamid ya bayyana ma almizan shi   ne gina tarbiyyar ‘ya’yan  shahidai  a tafarkin da iyayensu  suka sadaukar da rayukansu  tare da wayar masu da kawunansu akan muhimman wurare na tarihi dake cikin wannan kasa. 

Saturday, February 18, 2012

YADDA AKA GABATAR DA TARON KARA MA JUNA SANI NA 'YANUWA 'YAN KASUWA A KATSINA

Kadan daga cikin hotunan da aka dauka yayin gabatar da taron karama juna sani na kwana biyu da 'yanuwa 'yankasuwa suka shirya a katsina, kwanakin baya.

Daga: AbdulAzizi




















Saturday, February 11, 2012

A CI GABA DA BUKUKUWAN MAULUDIN MANZON ALLAH, AN GABATAR DA FARETI A KATSINA

Akaro na biyu, Lajnar Islamiyyu ta harkar musulunci dake da’irar Katsina da kewaye, ta kaddamar da gasar farertin girmamawa ga Manzon Allah (S) na wannan shekara a ranar Assabat 19/3/1433, a Unguwar filin samji dake Katsina.
Makarantun islamiyyu, daga sassa daban-daban ne suka halarci wannan gasa, cikin makarantun da suka shiga wannan gasa, akwai Fudiyyoyin, Batagarawa,Magamar Jibiya,Rimi Abukur, Bindawa,sai Islamiyyu irinsu Baharul’Fatimiyya,Shabbabul’Mahadi,Tarbiyyatul’islam da sauransu,inda kowace makaranta ta fito ta gabatar da irin shirin da take da shi da zaya kayatar da faretin.
A jawabin da ya gabatar bayan Kammala wannan gasa, Malam Yakubu Yahaya Wakilin ‘yanuwa na Katsina, ya Godema daliban Makarantun ,malamansu tare da wadanda suka koyar da su irin wannan Fareti . Malam Yakubu ya bayyana cewa, irin duk abinda mutum zaya gabatar da zaya nuna murna ga samuwar Manzon Allah , to halal ne matukar ba ya sabama koyarwar Musulunci ba ne.Ya ce, ga masu ganin an zurfafa ga son Manzon Allah kuwa, “sai su nuna mana iyakar darajar Annasbi, mu kuma mutsaya a nan”.Daga nan sai ya kirayi iyaye da su kula sosai akan tarbiyyar ‘ya’yansu, musamman a wannan lokaci da makiya suke kirkiro da wasu hanyoyi na lalata tarbiyyar ‘ya’yan musulmi. Ga wadanda ‘ya’yansu suke da wayoyi kuwa ,ya kiraye su da su rika kulawa da irin abubuwan da suke cikin wayoyin yaran nasu don sanin halinda suke a ciki, sai ya ce mafita daga irin wannan tarko shine kusantar Allah (T) da ibadu tare da aza yaran bisa tsayuwa da ibadun,Ya yi nuni da cewa ,kada kaga yaranka yana karatu,wannan bai isa ba sai an kula da irin abokan da suke tare da su.
Ita dai wannan gasa ta fareti a tabakin Malam Yakubu Idris wanda shine shugaban Lajnar ta Islamiyyu, cewa ya yi, an shirya wannan gasa ce, domin girmamawa ga Manzon Allah(S) kuma wannan sababben abu ne cewa, idan wani wanda ake girmamawa ya kai ziyara a wasu kasashe, to ana shirya masa fareti, saboda haka wannan Lajna ta tsara gabatar da shi domin girmama Manzon Allah(S).
Makarantunn da suka samu nasara a wannan gasa ta bana, sune, Fudiyya Batagarawa a matsayin ta hudu, Baharul Fatimiyya ta uku, Fudiyyah Rimi ta biyu sai Tarbiyyatul Islam Marnar Kadabo matsayin wadda tazo zakara watau ta daya.
Ashekarar da ta gabata ne dai aka fara gabatar da irin wannan gasa a cikin tsare-tsaren bukukuwan Mauludi. An dai kamala gasar cikin nasara da farin ciki daga al’ummar da suka sami halarta. 














Saturday, January 21, 2012

DANDALIN MATASA NA YANKIN KANO YA ZIYARCI NA KATSINA


 
A ranar  Laraba ne  25/ n2/ 1433 A.H,tawagar ‘yanuwa na Dandalin matasa na yankin Kano, suka kawo ziyara ga takwarorinsu da ke  Katsina domin sada zumunci tare da gabatar da jawabai na karfafa juna.
A jawabin da ya gabatar , shugaban dandalin na matasan harkar musulunci a karkashin jagorancin Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) Malam Hafizu Dauda  Kano, ya ankarar da ‘yanuwa matasa na gwagwarmaya akan manufar wannan ziyara , inda yace,domi sada zumunci ne da tattauna yadda za a iya haduwa a  karfafa juna , sai  ya ce, akwai bukatar kowanensu ya kula da kansa ta hanyar  siffatuwa  da kyawawan dabi’u, ganin cewa a yanzu akwai gurbacewar  tarbiyya. Ya kuma ya karfafi  ‘yan  dandalin da suci gaba da nemo malaman harka, ko masana su  rika yi masu bayani akan wasu bangarori na harka, ya kuma yi kira ga Malaman harkar nan da kara sa kula su fahinci matsalolin matasan domin a shigowa  da magancce su.
A wani sashen jawabin , Malam Hafizu ya tunanatar da ‘yanuwan cewa,Sayyid (H)  ya bayyana matasa a maatsayin jari na wannan harka,sai ya nuna wajabcin siffantuwa da kyawawan ayyuka  kamar  yadda Sayyid din yake koyarwa, sannan ya  bukaci matasan su kauce ma munanan ayyuka da za su jawo suka ga wannan kira da Sayyid din ke ma jagoranci. ya kuma bukaci matasa su kara kulawa da al’amurran harka ta hanyar nazartar tarihinn kiran, yaddad  harkar ta taso da irin sadaukarwar da magabatanta suka yi  domin samun damar tsayuwa akan ta.Sai yayi kira akan dagewa da ibada ta hanyar azumomi da sallolin na da makamantansu. A karshen jawabin nasa, ya bukaci kowane matashi ya zamo yana da wata gudunmuwa da yake bayarwa a wannan harka domin ta ci gaba.
A nasa  jawabin, danuwa Sanusi  Idris Musa, jawo hankalin matasa ya yi ta hanyar nuna takaicin  yadda suke wahalar da maluman harka  ta yin watsi da shiryarwar da suke yi a kodayaushe, sai  ya bukaci matasan su sa tunani tare da nazartar maganganun  Maluman, da kuma yin aiki da su.Ya ce  koda  kashi Hamsin cikin Dari na maganganunsu  aka yi aiki da su, to  da an ga sauyi a rayuwar  matasan. Ya shawarci matasan da cewa, kowanensu ya  duba  ya ga inda yake da gajiyawa ya yi aiki domin gyara matsalarsa saboda ana yin wannan harka ne domin neman  yardar  Allah(T).
Malama Fatima Yusuf Ali , daya  daga cikin wadanda suka kawo ziyarar daga Kano, ta bukaci ‘yanuwa maza da mata da su himmatu akan neman sanin ilmomi tare da sanin ilimin computer da harkar internet  domin yada  da’awar  Malam (H),ta kuma  jawo hankali akan dagewa  dai  da mujahada  domin iya tunkarar halin da ake ciki a yanzu haka.

A jawabin godiya da ya gabatar, Shamsuddin  Ahmad  a madadin ‘yan dandalin na yankin  Katsina, ya nuna godiya  ga , maziyartan da wannan  ziyara da suka kawo masu , ya kuma yi fatan su ‘yan kwamitin za su yi amfani da duk abubuwan da suka ji a wannan zama.
An kammala wannan ziyara cikin nasara, kuma tuni bakin suka isa gida lafiya.