Saturday, February 18, 2012

YADDA AKA GABATAR DA TARON KARA MA JUNA SANI NA 'YANUWA 'YAN KASUWA A KATSINA

Kadan daga cikin hotunan da aka dauka yayin gabatar da taron karama juna sani na kwana biyu da 'yanuwa 'yankasuwa suka shirya a katsina, kwanakin baya.

Daga: AbdulAzizi




















Saturday, February 11, 2012

A CI GABA DA BUKUKUWAN MAULUDIN MANZON ALLAH, AN GABATAR DA FARETI A KATSINA

Akaro na biyu, Lajnar Islamiyyu ta harkar musulunci dake da’irar Katsina da kewaye, ta kaddamar da gasar farertin girmamawa ga Manzon Allah (S) na wannan shekara a ranar Assabat 19/3/1433, a Unguwar filin samji dake Katsina.
Makarantun islamiyyu, daga sassa daban-daban ne suka halarci wannan gasa, cikin makarantun da suka shiga wannan gasa, akwai Fudiyyoyin, Batagarawa,Magamar Jibiya,Rimi Abukur, Bindawa,sai Islamiyyu irinsu Baharul’Fatimiyya,Shabbabul’Mahadi,Tarbiyyatul’islam da sauransu,inda kowace makaranta ta fito ta gabatar da irin shirin da take da shi da zaya kayatar da faretin.
A jawabin da ya gabatar bayan Kammala wannan gasa, Malam Yakubu Yahaya Wakilin ‘yanuwa na Katsina, ya Godema daliban Makarantun ,malamansu tare da wadanda suka koyar da su irin wannan Fareti . Malam Yakubu ya bayyana cewa, irin duk abinda mutum zaya gabatar da zaya nuna murna ga samuwar Manzon Allah , to halal ne matukar ba ya sabama koyarwar Musulunci ba ne.Ya ce, ga masu ganin an zurfafa ga son Manzon Allah kuwa, “sai su nuna mana iyakar darajar Annasbi, mu kuma mutsaya a nan”.Daga nan sai ya kirayi iyaye da su kula sosai akan tarbiyyar ‘ya’yansu, musamman a wannan lokaci da makiya suke kirkiro da wasu hanyoyi na lalata tarbiyyar ‘ya’yan musulmi. Ga wadanda ‘ya’yansu suke da wayoyi kuwa ,ya kiraye su da su rika kulawa da irin abubuwan da suke cikin wayoyin yaran nasu don sanin halinda suke a ciki, sai ya ce mafita daga irin wannan tarko shine kusantar Allah (T) da ibadu tare da aza yaran bisa tsayuwa da ibadun,Ya yi nuni da cewa ,kada kaga yaranka yana karatu,wannan bai isa ba sai an kula da irin abokan da suke tare da su.
Ita dai wannan gasa ta fareti a tabakin Malam Yakubu Idris wanda shine shugaban Lajnar ta Islamiyyu, cewa ya yi, an shirya wannan gasa ce, domin girmamawa ga Manzon Allah(S) kuma wannan sababben abu ne cewa, idan wani wanda ake girmamawa ya kai ziyara a wasu kasashe, to ana shirya masa fareti, saboda haka wannan Lajna ta tsara gabatar da shi domin girmama Manzon Allah(S).
Makarantunn da suka samu nasara a wannan gasa ta bana, sune, Fudiyya Batagarawa a matsayin ta hudu, Baharul Fatimiyya ta uku, Fudiyyah Rimi ta biyu sai Tarbiyyatul Islam Marnar Kadabo matsayin wadda tazo zakara watau ta daya.
Ashekarar da ta gabata ne dai aka fara gabatar da irin wannan gasa a cikin tsare-tsaren bukukuwan Mauludi. An dai kamala gasar cikin nasara da farin ciki daga al’ummar da suka sami halarta. 














Saturday, January 21, 2012

DANDALIN MATASA NA YANKIN KANO YA ZIYARCI NA KATSINA


 
A ranar  Laraba ne  25/ n2/ 1433 A.H,tawagar ‘yanuwa na Dandalin matasa na yankin Kano, suka kawo ziyara ga takwarorinsu da ke  Katsina domin sada zumunci tare da gabatar da jawabai na karfafa juna.
A jawabin da ya gabatar , shugaban dandalin na matasan harkar musulunci a karkashin jagorancin Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) Malam Hafizu Dauda  Kano, ya ankarar da ‘yanuwa matasa na gwagwarmaya akan manufar wannan ziyara , inda yace,domi sada zumunci ne da tattauna yadda za a iya haduwa a  karfafa juna , sai  ya ce, akwai bukatar kowanensu ya kula da kansa ta hanyar  siffatuwa  da kyawawan dabi’u, ganin cewa a yanzu akwai gurbacewar  tarbiyya. Ya kuma ya karfafi  ‘yan  dandalin da suci gaba da nemo malaman harka, ko masana su  rika yi masu bayani akan wasu bangarori na harka, ya kuma yi kira ga Malaman harkar nan da kara sa kula su fahinci matsalolin matasan domin a shigowa  da magancce su.
A wani sashen jawabin , Malam Hafizu ya tunanatar da ‘yanuwan cewa,Sayyid (H)  ya bayyana matasa a maatsayin jari na wannan harka,sai ya nuna wajabcin siffantuwa da kyawawan ayyuka  kamar  yadda Sayyid din yake koyarwa, sannan ya  bukaci matasan su kauce ma munanan ayyuka da za su jawo suka ga wannan kira da Sayyid din ke ma jagoranci. ya kuma bukaci matasa su kara kulawa da al’amurran harka ta hanyar nazartar tarihinn kiran, yaddad  harkar ta taso da irin sadaukarwar da magabatanta suka yi  domin samun damar tsayuwa akan ta.Sai yayi kira akan dagewa da ibada ta hanyar azumomi da sallolin na da makamantansu. A karshen jawabin nasa, ya bukaci kowane matashi ya zamo yana da wata gudunmuwa da yake bayarwa a wannan harka domin ta ci gaba.
A nasa  jawabin, danuwa Sanusi  Idris Musa, jawo hankalin matasa ya yi ta hanyar nuna takaicin  yadda suke wahalar da maluman harka  ta yin watsi da shiryarwar da suke yi a kodayaushe, sai  ya bukaci matasan su sa tunani tare da nazartar maganganun  Maluman, da kuma yin aiki da su.Ya ce  koda  kashi Hamsin cikin Dari na maganganunsu  aka yi aiki da su, to  da an ga sauyi a rayuwar  matasan. Ya shawarci matasan da cewa, kowanensu ya  duba  ya ga inda yake da gajiyawa ya yi aiki domin gyara matsalarsa saboda ana yin wannan harka ne domin neman  yardar  Allah(T).
Malama Fatima Yusuf Ali , daya  daga cikin wadanda suka kawo ziyarar daga Kano, ta bukaci ‘yanuwa maza da mata da su himmatu akan neman sanin ilmomi tare da sanin ilimin computer da harkar internet  domin yada  da’awar  Malam (H),ta kuma  jawo hankali akan dagewa  dai  da mujahada  domin iya tunkarar halin da ake ciki a yanzu haka.

A jawabin godiya da ya gabatar, Shamsuddin  Ahmad  a madadin ‘yan dandalin na yankin  Katsina, ya nuna godiya  ga , maziyartan da wannan  ziyara da suka kawo masu , ya kuma yi fatan su ‘yan kwamitin za su yi amfani da duk abubuwan da suka ji a wannan zama.
An kammala wannan ziyara cikin nasara, kuma tuni bakin suka isa gida lafiya.
   

Tuesday, December 6, 2011

AN GABATAR DA MUZAHARAR JUYAYIN ASHURA TA SHEKARAR 1433 A KATSINA


A wannan rana ce ta Talata 11 / 1/ 1433, ‘yanuwa musulmi almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) a karkashin jagorancin Malam Yakubu Yahaya  Katsina kamar sauran takwarorinsu na duniya, suka gabatar da Muzaharar juyayi da nuna bakin ciki akan kisan da Yazidawa makiya zuriyar Manzon Allah suka yi ma Imam Husaini Dan Ali dan Abi Dalib Dan Fatima diyar Manzon Allah (S) da zuriyarsa tare da abokansa a filin karbala.

A jawabin da ya gabatar bayan kamala wannan  gagarumar muzahara, Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa na garin Katsina, ya bayyana  cewa, manufar wannan jerin gwano shine jajantawa tare  mika ta’aziyya ga Manzon Allah(S), Imamul Asr(AJ), Sayyi Ali Khaminei da Sayyid Zakzaky(H) da sauran bayin Allah.Ya ce , mika  wannan ta’aziyya  duk duniya ne ake  yi ba nan kawai bane kamar yadda wasu suke dauka, ya ce , zaman makoki da irin wannan muzahara duk ta’aziyya ce zuwa ga Manzon Allah, domin shine wanda aka cutar, kuma wannan ya faru tun bayan wafatinsa.ya kara da cewa, bayan wannan ta’addanci ,an tafi  da zuriyar Manzon Allah mata da kananan yara  da suka  yi saura daga filin Karbala  zuwa Sham fadar Yazidu dan Mu’awiyya (LA) a kasa ana tafe ana tozarta su a duk garin da aka wuce ta cikinsa. ya ce, sakamakon wannan ta’addanci ne Allah ya sallada  ma musulmi Kaskanta  a hannun Magolawa kafiarai  abin da ya tafo har wannan zamani da musulmi suke cikin kaskancin Kafiran duniya.

Sannan ya ce, lokacin dawowar musulmi akan lamarinsu na addini ya yi,domin addinin ne zaya hada su waje daya. Sai ya ce, dole ne abinda ya dami Manzo ya dame ka, kuma dole ne ranar bakin cikinsa kaima ta zama rana ce ta bakin cikinka idan dai har Manzon kake bi kai ba munafuki bane ba kai
.
Malam Yakubu ya nasihanci masu sukar abinda muke yi da ganin ba daidai bane, da su binciki littattafansu indai har da gaske suke yi ba munafunci bane.Ya kara da cewa, Allah ya kawo lokacin da za’a gane abinda aka yi ma wadannan bayin Allah, kuma ko bamu nan  ga ‘ya’yanmu nan zasu ci gaba da wannan al’amari.”Ya nasihanci malamai da su ji tsoron Allah, su tsaya ma gaskiya domin jama’a suna kallonsu, ya ce “wannan lamari na Shi’a yazo zama ne”.

Ya kuma ja kunnuwan mahukunta dake hankoron hanawa ko afkama wannan lamari da cewa,”wannan Shi’a din ita ce ajalin gwamnatin wannan kasa, sai ya gargade su da cewa”su ja bakinsu su tsuke, su sama wannan al’amarin  ido, “idan kuma kuka ce ba haka ba,  za ku yi rigima ne da al’umma, domin al’umma adalci take so kuma a addini ne ake samunsa,  ya kuma ce,” babu wanda zaya fahimci wannan gida na Annabi, sannan ya rabu da shi . “idan ba za ku zo ayi da ku ba, kusa ido.Kawo jami’an tsaro da kuke kokarin yi  kuma ku yi ta kawowa, kuna amfani da zahirine shi kuma Allah yana amfani ne da zukata.

 Ya kare da cewa, da Imamu Husaini bai tashi ba da yanzu ba addini ne ake yi ba , domin su Umayyawa sun shirya maido da Jahiliyyar da Manzon Allah ya kawar ne, mikewar Imam it ace ta tsaida su.

Ita dai wannan muzahara, dubunbubatar ‘yanuwane maza da mata da kananan yara suka gabatar da ita a cikin yanayi na juyayi da nuna bakin cikin abinda aka yi ma zuriyar Manzon Allah bayan rasuwarsa.









Friday, December 2, 2011

WASU DAGA CIKIN HOTUNAN KARATUN ASHURA DA MALAM YAKUBU YAHAYA KE GABATRWA NA WANNAN SHEKARA TA 1433











DA'IRAR 'YANUWA MUSULMI TA KATSINA TA FARA GABATAR DA KARATUN JUYAYIN ASHURA NA SHEKARAR 1433 A.H

A ranar Assabat 1/1/1433 ne, Da’iarar ‘yanuwa musulmi almajiran Sayyid Zakzaky(H) ta Katsina  karkashin jagorancin Malam YakubuYahaya ta fara zaman makokin domin jajanta ma Manzon Allah (S) akan kisan da  makiya suka yi ma jikokinsa a Karbala.

A gabatarwar da ya yi kafin fara karatun,  Malam Yakubu ya ce, manufar wannan zama na makoki shine jajanta ma Manzon Allah(S), A’imma(AS) dasauran bayin Allah managarta akan zagayowar wannan musiba domin dole ne son Iyalan Manzon Allah saboda irin al’khairan da ya zo ma al’umma  da shi”dole ne ka nuna farin cikinka  akan duk abinda ya faranta ma Manzo da Iyalansa, haka kuma, wajibi ne nuna bakin ciki kan duk abinda ya bakanta masu” sai ya bukaci jama’a da basu fahimci abin da muke yi ba su bamu uzuri domin muna sauke wajibin da ya hau kanmu ne.”Malam Yakubu ya yi nuni da cewa,”zamu bi salon da muka saba bi ne na karanta littafan magabata domin sauran jama’a da zasu saurara suma su amfana” sannan ya ce,dukkan abinda ya faru  a wannan waki’a, ba kire bane ba kuma kage, sai dai muna karantawa ne daga littafai da aka rubuta su tsawon shekaru kuma a mabambantan garuruwa da zamunna domin mu amfana da  tarihi, don yin aiki da kyawawan dabi’u da watsi da munana.”

Malam Yakubu ya tabo tarihin gasar dake tsakanin Kuraishu da Hashimawa da yadda Hashimawa suka yi fice, abin da ya sa sauran Kabilun suka nuna masu gaba da kiyayya musamman wadda Umayyawa suka nuna abinda ya tafo har zuwan musulunci sannan bayan yakokin da Manzon Allah ya jagoranta wanda Imam Ali(AS) ya kashe mayan kafiran Kuraishu, sai gabar ta karu tsakainsu da Zuriyar Annabi abinda ya yi sanadiyyar kisan gillar da Yazidu (L) ya yi ma Imam Husain(AS) da zuriyarsa da magoya bayansa a Karbala domin ya dauki fansa.

 Kafin nan,sai da Malam Yakubu ya karanto tarihin da ke nuni da cewa, asalin Abdussamshi wanda ya  haifi Umayyam, mutumen Rum ne da aka kamo sa a matsayin bawa daga bisani aka mayar da shi da -ta hanyar Tabanni-
sannan shi kuma   Mu’awiyya ba dan Abu Sufyanu ba ne na hakika sai dai da ne ga wani da ake ce ma Musafiru wanda ya samar da cikinsa ta hanyar nema dake tsakaninsa da Hindu,wadda abu sufyanu ya aure ta bayan samun cikinsa.

Sanna ya bukaci jama’a su binciki tarihidomin sanin gaskiyar abinda ya faru tare da sanin asalin gabar su Abu-Sufyanu da Zuriyar Manzon Allah(AS).

Ya yi fatan za a kamala wannan zama tare da fatan wannan jaje ya zama karbabbe gami da fatan tabbata a wannan harka ta Musulunci.