Monday, May 30, 2011

YANKIN SHAHID HAMZA YA GABATAR DA TARON KARAWA JUNA SANI NA WUNI DAYA

mediaforumkatsina
A ranar Lahadi 26/6/1432 ne, yankin Shahid Hamza na Mu’assasatus Shuhada’u shiyyar Katsina da kewaye shirya taron bita na wuni daya a Markazin ‘yanuwa musulmi dake Katsina ga ‘yanuwa dake dauke da masa’uliyyar tattaro hakkin shahidai, da niyyar ankarar da su nauyin day a rataya a wuyansu.


Malam Ibrahim Potiskum, ya jawo hankalin ‘yankwamitin da cewa , batun karbo infakin shahidai, babban aiki ne da ya doro akan ‘yan kwamitin sannan aiki ne mai falala, inda ya tabo muhimmancin kulawa da da ‘ya’yan shahidai tare da kulawa da tarbiyyarsu abinda ya alakanta da tattaro wadannan hakkoki na shahidai.Sai ya jawo hankalin ‘yan kwamitin da su kara kokari wajen sauke nauyin shahidan da iyalansu ta hanyar dagewa wajen karbo wadannan kudade a hannun ‘yanuwa ,ya yi kira ga ‘yanuwa da su fahimci muhimmancin wadannan hakkoki na shahidai ta hanyar biyan nasu da na iyalansu baki daya, inda ya kara da cewa, abin koyinmu Sayyid Zakzaky(H) haka ya yi a lokacinda kwamitin shuhada’u ya kai Masa ziyara, kuma ya biya na shekara ne baki daya. Ya kuma yi kira ga wakilan mu’assasa da su zama masu bayarda nasu hakkokin dunkule a farkon lokaci domin samun nasarar ayyukansu, bai dace ba kaje karbar kudin wani ba tre da ka sauke naka nauyinba.

A dan takaitaccen jawabin da ya gabatar, Dakta Mustapha Sa’id wanda yana daga cikin masu jawabi, ya yi kira ne da a kara dogewa wajen fadakar da ‘yanuwa muhimmancin sauke wannan nauyi na hakkin shahidai,inda yace kada a gajiya, domin al’amarin yana bukatar aita fadkarwa har jama’a su fahinci muhimmancin infakin na shahidai.

A nasa jawabin,Malam Shehu Dalhatu ya fara ne bayyna ma’anar Mas’uliyya da cewa aba ce dake nufin wani nauyi da aka dora maka , sannan yace kuma ita mas’uliyaabin tambayace;idan ba zaka iya ba,to ya kamata ka bayyana,ya ce wannan aiki na tara hakkin shahidai abu ne mai muhimmanci, kuma kin karbowa saryarda hakkin shahidai ne. Ya kara da cewa wannan wakilci na Malam a cikin ‘yanuwadomin shi ne ya samar da wannan mu’assasa ta shahidai.” Ya kara da cewa,”yi ma ‘ya’yan shahidai hidima yi ma shahidin ne domin shi maraya ne kuma yi masa hidima ba karamar falala bace, inda ya karfafa magananarsa da kawo kissoshin wasu da suka ciyar da dabbobi suka samu rahama da kuma wadda ta azabtar da kyanwa ta shiga wuta. Sai ya yi kira ga ‘yanuwa das u auna tsakanin wadannan domin su fahinci falala ta wannan aiki na tara hakkin shahidai.ya yi kira ga ‘yankwamitin das u rika karama ‘yanuwa haske da bayanai da suke samu daga Bakunan su sayyid Zakzaky(H), domin suna samun bayanai da sauran ‘yanuwa basa samu, kuma wannan zaya taimaka wajen kara fahimtar wannan lamari.Sai ya yi kira ga wakilan kwamitinda su yi aiki tukuru domin samun nasara.

A tun farko said a wakilai daga wasu garuruwa, suka bayar da rahotannin yadda suke gabatar da ayyukan nasu abin da ke da bukatar tashi tsaye daga wakilan ‘yanuwa na garuruwa wajen wayar ma ‘yanuwa kai a kodayaushe domin fahimtar wannan nauyi tare da sauke shi domin cimma abiubuwan da aka sa agaba.

Shidai wannan mu’utamar an tattauna ne akan bayanai da suka hada da ,ayyukan mu’assasa da kalu bale da ke akan yankwamitin,sai muhimmancin sauke mas’uliyya da kuma hanyoyin bunkasa kudin shiga(hakkin shuhada). Tuni dai aka kamala wannan taro kuma baki suka koma garuruwansu dauke da niyyar aiwatar da abubuwan da aka tattauna a wannan taro.

No comments:

Post a Comment