Da ya juya akan al’amarin wannan harka da Sayyid Zakzaky(H) yake yi ma jagoranci, Malam Yakubu ya bayyana cewa, wannan harka it ace lasisin na yanke matsalolin Lahira,kuma wannan harka ta ginu ne bisa yakini kuma ta faro ne daga tushe ,karancin ilmin al’umma da kuma malamai da muke rayuwa tare dasu ,suna suna gai ana iya yin addini ko yaya sako-sako duk yadda ya samu ba komi. sai ya nuna cewa addini ya umurci mutum ya tsayu ne kyam akansa kada mutum ya karkata zuwa ga azzalumai”ka tsayu kamar yadda aka umurce ka kada ka yi shisshigi, kuma kada ku karkata ga wadanda suka yi zalunci ma kawunansu sai ku shiga wuta tare da su” sai ya yi gargadin bin azzalumai masu tsara ma mutane dokoki sabanin na Allah(T) kuma yace wannan aya ta hada da wadanda suka yarda da sakon manzo domin ta nuna “da wadanda suka tuba tare da kai”.sai ya kara da cewa, bisa dabi’a wadanda suka yi riko da addini ya yi istikama , to abinda ya sami na farko na shahada da abinda ya sami wannan bawan Allah, Alhaji Ibrahim zaya same shi domin ba a kashe su ba sai saboda addinsu.”kowane alhairi akwai na sama das hi har sai an kasha mutum saboda Allah ,to wannan shine alkhairin da babu na sama da shi.”kamar yadda ya malam Yakubu ya karanto.Ya yi fatan Allah ya arzuta mu da samun shahada a wannan tafarki na musulunci.
Taron ya sami halartar Malam Yakubu Yahaya da ‘yan kwamitin mu’assasatus shuhada’u daga Zariya, dakta Mustapha Sa’id da Malam Ibrahim Potiskum da shugaban kwamitin na Katsina Malam Ahmad Abbas da wasu daga cikin ‘yankwamitin sai kuma kwamitin ah –ludduthur na yankin a karkashin jagorancin MAlam AbdulKarin Usama.
A jawabin da Malam Yakubu Yahaya ya gabatr saboda yanayin ruwan sama da aka tabka,
Malam Yakubu ya bayyana shahada da cewa babban matsayi ne da Allah yake ganin zuciyar mutum abinda ta kudurce wanda shi kadai ya sani sai ya arzuta shi da ita, ya kawo darajoji na shahidi,sannan ya gargadi ‘yanuwa da su tsayu kyam akan addini ko kadan kada a karkata ga azzalumai”kada ku karkata ga azzalumai sai wuta ta shafe ku sannan ba za a taimakeku ba” kamar yadda yake a littafin Allah al’kur’ani.Sai malam yakubu
No comments:
Post a Comment