Monday, January 31, 2011

BA A ZABI MUSULMI BA NE MAFITA SAI DAI KOMA MA BIN TSARIN MUSULUNCI



An bayyana cewa ba a tallar gaskiya ta hanyar yin amfani da barna,amma dai ana tallar gaskiya ne da gaskiya.Malam Yakubu Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da wa’azin mauludin Annabi (SAW) da yankin zone © suka shirya aka gabatar a Tudun Matawalle Sabuwar Unguwa Katsina.



Malam yakubu ya ci gaba da bayyana cewa, ta hanyar da Manzon Allah ya shata ne kawai zaka iya kawo Addini bata hanyar a zabi Musulmi da wasu Malamai suke ta yekuwa ba.ya ce, “ai Manzon Allah an yi masa tayi na shiga tsarin gwamnatin Kuraishu,amma bai shiga ba.”da ta haka ake taimakon Addini, da Manzon ya karba wannan tayi” ya gargadi musulmin kasar nan da su yi hattara da wutar rikici tsakanin musulmi da kafirai da ake yayatawa a halin yanzu ta hanyar cewa, a zabi musulmi ba kafiri ba, domin dai duk tsarin ba musulunci bane. Ya ce, kuma ko an yi rigima tsakanin musulmi da kafirai a kasar nan, to babu wata nasara da musulmin za su samu domin Allah baya taimakon komi sai gaskiya. Kuma wani makirci ne ake kitsawa da nufin bada dama kafiran duniya su kafa sansaninsu a wannan yanki na musulmi da niyyar kwasar arzikin da Allah ya aje shimfide a bayan wannan kasa” wannan tarko ne da aka dana ma musulmin wannan kasa, matukar basu koma ma addini ba akwai matsala”



Malam yakubu ya karyata masu cewa yin rajista da zaben musulmi a wannan tsarin Jihadi ne.ya ce , “idan kuwa jihadi ne, to da Manzon Allah da Sahabbansa duk kuskure suka yi kenan ,Waliyazu bil’Lahi” Sannan yace,”kifar da gwamnatin zalunci da mayar da tsarinta na Addini shjine mafita ba rudanin a zabi musulmi ba.”

DA'IRAR KATSINA DA KEWAYE TA GUDANAR DA TARON YINI DAYA DA NUFIN ZABURANTAR DA 'YANUWA DOMIN KAWATA MAULUDIN MANZON ALLAH

A ranar Alhamis 23/2/1432 ne, Da’irar yanuwa Musulmi almajiran Sayyid zakzaky(H) ta Katsina, ta gabatar da taron yini daya da nufin samar da kyakkyawan tsari da zaya kayatar da bukukuwan mauludin ManzonAllah (SAW) na wannan shekara a karkashin jagorancin wakilin ‘yanuwan na yankin Katsina Malam Yakubu Yahaya a markaz da ke garin Katsina.
A taron, Mallam Yakubu ya bukaci ‘yanuwa da suke a Halkoki da su dinga gudanar da bukukuwan Mauludodin bayin Allah da halkokin suke dauke da sunayensu a duk lokacin da ranar haifuwar wannan bawan Allah ta zagayo. Sannan kuma su ‘yanuwan su fadada kyaututtuka da suke bayarwa ga bangarorin al’umma kamar marayu, tsofaffi, Sharifai zta hada da guragu Kutare da sauran makamantansu.Harwala yau, Malam yakubu ya bukaci ‘yanuwa da su kara shiri domin kayatar da bukukuwan murnar zagayowar watan haifuwar manzon Allah na wannan shekara.
A wannan taron dai, sai da kowane bangare ya tashi ya bayyana irin shirin da yake tsarawa da niyyar a karu da tsare-tsaren juna domin dai bukukuwan maulidin na bana su kayatar.
Damadai halkokin na wannan yanki suna dauke ne da kodai sunayen A’imma (AS) ko kuma sunan Manzo, Iyayensa Da sauran bayin Allah Mujaddadai da waliyyan
Allah maza da mata da suka ba wannan addini gagarumar gudun muwa.
An dai kammala wannan taro cikin nasara, kuma tuni shirye-shirye sun riga sun kankama na ganin nasarar mauludin Annabi (SAW) na wannan shekara.

Sunday, January 9, 2011

ISMA TA GABATAR DA KACIYA GA KANANAN YARA A WANNAN SHEKARA

Daga: AbdulAzizi
Bangaren kiwon lafiya na harkar Musulunci da Sayyeed Ibrhim Zakzaky(H) yake yi ma jagoranci da ke yankin Da’irar Katsina da kewaye ya kwashe mako uku yana gabatar da kaciyama yara a markazin ‘yanuwa dake cikin garin na katsina.


Aikin wanda aka fara gabatar da shi tun a ranar Assabat 20 ga watan al’Muharram 1432, ana cigaba da yinsa a duk ranakun Assabat da Lahadi.

Yusuf AbdulLahi ya bayyana cewa, Sashen na kiwon lafiya da ke karkashin harkar ta Islamiyya,yana gudanar da wannan kaciyar ne domin taimaka ma alumma kamar yadda Sayyeed Zakzaky(H) yake shiryarwa akan tallafa ma jama’a.

Kimanin yara sittin ya zuwa yanzu aka yi ma wannan kaciya, kuma har yanzu ana ci gaba da aiwatar da ita.

Shidai wannan aiki na kaciya sashen ya saba gabatar da shi, a duk shekara.

DANDALIN DALIBAI NA YANKIN KATSINA YA GABATAR DA DAURA TA KWANA HUDU

Daga:Abdul'Azizi
Dandalin dalibai na harkar Musulunci na yankin katsina, ya gabatar da taron karama juna sani da ya saba shirya ma dalibai da suke karatu a matakai daban-daban na Ilimi musamman makarantun gaba da primary a duk lokutan huto. wannan taro an gabatar da shi ne a harabar Makaratar Fudiyyah dake Unguwar Sabuwar kofa Katsina.


A taron an gabatar da darussa wadanda suka fi ba daliba dalibai wahala da suka hada da:Lissafi ,turanci science da sauransu a bangaren karatun boko,sai kuma abinda ya shafi darussan Addinin Musulunci, gami da ankarar Da su daliban abubuwan da suke faruwa a rayuwar yau da kullum a duniya baki daya.

Malam Isma’ila Yahuza wanda shine shugaban wannan dandali ,ya bayyana cewa, ana gabatar da wannan taro ne a duk lokutan hutu da niyyar kara horar da su daliban abubuwan da suka shafi karatunsu ,sannan a sanar da su abinda ya shafi Addini da wannan harka ta Musulunci da su Sayyeed Zakzak(H) yake yi ma jaagoranci, sannan a fadakar da su hikimomi da ya kamata su yi amfani da su a makarantu koda sukan sami kansu cikin wata matsala irin ta makaranta, duk wannan da niyyar su sami abinda zasu rika daga fara karatun zango zuwa dawowa wani hutun.

Taron wanda aka fara gabatar da shi tun daga ranar Laraba 4/2/1432 da yazo daidai da 5/1/2011, ya sami halartar dalibai da dama, sannan Malamai da dama ne suka bada tasu gudunmuwar wajen karantar da su daliban don ganin an cimma nasarar da ake bukata.

An dai kammala wannan taro na karawa juna sani cikin nasara da amfanuwa ga duk wadanda suka sami halartarsa.
Wasu daga cikin Daliban da suka sami halartar Mu'utamar da aka shiya a katsina

YANKIN IMAM HASAN MUJTABA( AS) NA DA'IRAR KATSINA YA GABATAR DA MU'UTAMAR KARO NA BIYAR A GARIN WAGINI

Daga: AbdulAzizi

A karo na biyar ,yankin Imam Hasan Mujtaba(AS)dake karkashin Da’irar ‘yanuwa Musulmi al’majiran Sayyed Zakzaky(H)ta katsina ta gabatar da taron karawa juna sani a garin Wagini, karamar hukumar batsari ta jihar katsina.
Malam Sabo ATC tare da wakilin 'yanuwa na Wagini a Mu'utamar da aka gabatar a Yankin Imam Hasan Mujtaba(AS)
Kamar yadda aka tsara, Malamai takwas ne suka gabatar da jawabai a maudu’o’i daban-daban da suka hada da ,Ilmi,Mujahada,Kiyada ,Sadaukarwa da kuma Makoma,sannan Malam Yusuf Yamai ya gabatar da wa’azin dare a babban masallacin juma’a na garin.

A jawabin nasa,malam yusuf yamai, ya fadakar ne akan kalmar Shahada. Ya nuna cewa,ya kamata al’umma ta lura da abinda zaya gyara inganta wannan kalma ko bata ta. Ya ce, duk abinda ka ji ya sami wani Annabi na jarabawa tsakaninsa da wadnda aka aiko shi ,to sakamakon aiki da wannan kalma ce ta shahada, kisane ko kora daga gari.Sai ya yi nuni da cewa,mi ya sa a yanzu ake furta wannan kalma,amma babu wanio abu da yake faruwa na jarabawa kamar yadda ya faru ga magabata.

Malam Yusuf, ya bayyana cewa,babu yadda za a yi ka aikatawannan kalma ta shahada, sai ka sami mutum biyu.Watau Annabi da Allah ya aiko shi da sakon kalmar ,sai kuma shugaba mai hana abi sakon Annabin.ya ci gaba da cewa,Allah ya tsara tun azal cewa,akwai mai zowa da sako daga Allah,akwai kuma mai kawo ma sakon tarnaki.Sai ya e, dole sai kabi Annabi ko Wasiyyinsa ko kuma mujaddadaiko wanda suka wakiltar sannan zaka sami tsira a lahira.

Da yaker kara bayani dangane da masu ganin cewa shugabannin yanzu musulmi ne, sai ya bada misalin yaadda Shehu Usman dan Fodiyu ya fafata dada yumfa duk kuwa da cewa,shi yumfa Musulmi ne, hasalima al’majirin Shehu ne kafin ya zama Sarki ya dauki matakin hana Shehu da’awa.sannan ya yi nuni da sayyeed Zakzaky(H) a wannan lokaci da yake yunkurin kira da shugabannin yanzu suke ta yunkurin takura masa.sai ya kirayi Musulmi da su bi jagorancin da zaya kai su ga tsira sannan ya tsoratar akan rayuwa akan yin rayuwa babu shugaban da zaya kai mutum zuwa ga tsira gobe Kiyama, domin Shugabanci fa shine ma’anar kalmar shahada.

A jawabinda ya gabatar a madadin Malam yakub yahaya da bai sami halarta ba saboda wasu ayyukan na harka, ya yi kokarin karin bayanim akan darussan da aka gabatar a tsawon wadannan kwanaki, inda ya karfafa akan dagewa wajen neman Ilimi da aikin da shi kamar yadda maulana Sayyeed Zakzaky(H) yake ta ankararwa ,sannan ya koka akan yanda ‘yanuwa suka yi sanyi da Mujahada abinda ya ke kawo ma ‘yanuwa tsogunguma marasa tushe balle makama, sannan ya bukaci mahalartan da adawon ma wannan Mujahada tunda babu wata rana da mallam(H) ya ce a daina yi.ya yi fatan dukkan ‘yanuwa zasu dage domin samun tabbata abisa tafarkin da Malam (H) yake kira akansa.

A tun farko ,Malam Hamza Musa Wagin wakilin ‘yanuwa na gabri, ya nuna godiya da banhakuri ga mahalarta musamman da suka daure duk da yanayin sanyi da ake ciki,sannan ya yaba ma al’ummar wannan gari akan hadin kai da goyon baya da suka bayar domin ganin wannan Mu’utamar ya gudana cikin nasara.

Wani sashe na 'yanuwa da suka halarci Mu'utamar din da aka gabatar a Wagini



'Yanuwa mata a Mu'utamar da aka gabatar a Garin Wagini, katsina