Friday, April 17, 2015

KAMMALA MAULUDIN DIYAR MANZON ALLAH(S) A KATSINA



 A jiya Alhamis ne aka kawo karshen tarurrukan mauludin Fatima(AS) da 'yan'uwa mata  na Da'irar Katsina da kewaye suka shirya.

Malam Yakubu Yahaya ne ya rufe wannan biki da karanto wani yanki da Hudubar Sayyida da ta yi a gaban Halifar musulmi Abubakar bayan hana ta hakkinta da aka yi  bayan wafatin Manzon Allah(S).
 Ba muna jin dadin karanto abubuwan da suka faru bayan wafatin Manzon ba ne, sai dai muna karantawa don mu san inda gaskiya ta ke , mu yi riko da ita ,mu kuma ji inda karya ta ke, mu bar ma masu karyar  abinsu.Malam Yakubu a wajen karatun Kammala Mauludin Fatima da ‘yan’uwa mata suka shirya a katsina
A karshe Malam Yakubu ya yi fatan Allah ya karba mana ya tabbatar da mu bisa shiriya, ya kuma nuna mana na wsu shekaru masu zuwa. Ya kuma yi fatan Allah ya saka ma kowa da alheri musamman wadanda suka shirya  da kuma wadanda suka taimaka har abin ya yiwu.

DANDALIN MATASA NA KATSINA YA SHIRYA MAULUDIN FATIMA(AS) A CHARANCI,KATSINA

A jiya Alhamis ne aka gabatr da Mauludin Diyar Manzon Allah a garin Charanci. Malam Kasim Umar Sokoto ne ya zama babban bako a wannan wuri inda ya gabatr da jawabai masu matukar muhimmanci da amfanarwa. Ya tabo batutuwa da suka hada da takaitaccen Tarihin Haihuwar Fatima(AS) da dalilan da suka janyo Allah (T( ya yi ma Mnazo baiwa da wannan tsarkakakka.
Ga wasu daga hotunan wannan mauludi nan kamar yadda za a iya gani.




Wednesday, April 15, 2015

KARIN HOTUNAN ZAGAYEN MAULIDIN FATIMA(as) A KATSINA

Wasu hotunan zagayen mauludin diyar Manzon Allah(S) da aka gabatar yau Laraba a Katsina.

MUZAHARAR MAULUDIN FATIMA ZAHARA(SA) A KATSINA


yan'uwa mata gami da daliban Fufiyyoyi da islamiyyu hade da Harisawa sun gabatar da muzaharar murnar Mauludin Fatima diyar Manzon Allah(S) a wannan rana ta Laraba. An kuma fara gabatar da ita tun misalin karfe tara na safe.
Ga wasu  hotunan da aka dauka nan kamar yadda muzaharar ta wakana.



Thursday, April 2, 2015

AN FARA GABATAR DA MAULUDIN SAYYIDA ZAHARA (SA) A KATSINA

A jiya Laraba ne kwamitin 'yan'uwa mata na Da'irar Katsina da kewaye ya fara tgabatar da mauludin Sayyida Zahara Diyar Manzon Allah (s)na wannan shekara ta 1436.An fara gabatar da jawabi ne a Unguwar Kofar Bai Kusa da Korau Cinima da ke cikinbirnin Katsina, haka kuma a yau da dare ne za a gabatar da jawabin mauludin a Unguwar Rafin Dadi a bakin Asibitin Malam Barau.wanda Malam Abubakar Nuhu Talata Mafara zai gabatar.