Friday, November 15, 2013

AN GABATAR DA MUZAHAHARAR ASHURA A KATSINA



 Tun da sanyin safiyar wannan rana ta Alhamis ne ta 11/1/1435 hijiriyya, dubun dubatar al’ummar musulmi suka fara yi ma garin Katsina kabbara domin amsa kiran Sheikh Ibrahim Almagri(H) na gabatar da muzaharar Ashura don nuna jaje ga Manzon Allah da Iyalansa na kisan da  rundunar yazidu (L) ta yi ma Imam Husaini(AS) da sauran zuriyar Annabi(S) da kuma nSahabban Imam Husainin a karbala.
malam Yakubu ya mika ta’aziyyar ‘yanuwa  da suka halarci wannan muzahara ga Manzon Allah da iyalansa masu tsarki, sannan ya kuma mika wannan ta’aziyya ga jagororin gwagwarmayar duni a wannan lokaci haka kuma zuwa ga sheikh zakzaky(H). Daga nan ya bayyana  cewa,wannan abu da ya faru ga  iyalan Annabi(S) kiyayya ce ,inda ya tabo irin yadda Kuraishawa suka shiga musulunci akan dole bayan da suka ga an rinjaye su.”Suun shiga musulunci ne ganin babu yadda zasu  yi domin an rinjaye su, sai suka ga bari su shiga cikinsa  domin su bata addsinin” kawo maganar Abu- jahal da ya ce, ba suna tuhumar Muhammadu ba ne da wani aibu.Sai malam Yakubu y ace, watsi da wasicin manzon Allah ne da ya yi a Gadir da   aka yi , shi ne ya jawo hawan Yazidu dan Mu’awiyya mulkihar ya yi aika-aikar da aka yi.
Malam yakubu ya kara da cewa, bayan wannan kisan ne da suka yi ,sai aka yi kokarin kawo ruwayoyi da suke nuna matsayin wannan rana ta ashura domin rufe wannan aibu, ya ci gaba da cewa, an yi kokarin shafa ma wadannan mabarnata farin fenti aka wanke su aka ce ma su ne masu addinin gaskiya.sai y ace, wadannan karairayi duk na banu Umayya ne don su rufe laifin da suka yi ma Allah da manzo.Sai y ace, wannan abiun da muke yi ba wasa bane ba kuma yayi ba nedomin l;olkacin yayi ya wuce a wajen mu, saboda tun muna yi mu kadai har gas hi yanzu muna yi tare da jikokinmu,ddon haka addini muke ba wasa ba.

No comments:

Post a Comment