Monday, November 18, 2013

'YANUWA SUN BAYAR DA GUDUNMWAR JINI A KATSINA


Sadaukar da jini don bayarwa ga masu bukatarsa a irin wannan lokaci na nuna juyayin Ashura kamar zaburantarwa ne a gare mu, dokmin Imam Husaini (AS)ba jininsa kawai ya sadaukar ba, yama sadaukar da rayuwarsa ne gaba daya data iyalansa dama Sahabbansa.Malam Yakubu Yahaya  wakilin ‘yanuwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky(H) na katsina ya b ayyana haka a lokacin da yake tattaunawa da wakilinmu a yayin bayar da jini da ‘yanuwan suka yi albarkacin sadaukarwar Imam Husaini(AS).
  
Malam Yakubu yahaya ya bayyana cewa, “an san muhimmancin bayar da jini a wannan zamani, domin shi jini jigo ne a rayuwa, shi yasa ma zaka ga  ana farautar jini harma da kudi domin mutane su  samu su rayu, musamman yayin bukata, ko saboda haihuwa, hadari da makamantansu. Shi ya sanya masana suka muhimmantar da bayar das hi.”Sai ya karfafa bukatar bayar da jini muddin hakan zaya amfanar da dan Adam.
Ta fuskacin addini, malam Yakubu ya bayyana cewa, idan mutum ya bayar da jini aka ceto rayuwar mutum daya, ladar da zaya samu kamar ya ceto rayuwar al’umma ne baki daya.Ya karfafa maganar da ayar nan dake nuni da cewa, ‘wanda ya  kasha rai, kamar ya kasha rayuka ne baki daya, wanda ya raya rai daya, ,kamar ya raya rayuka ne gaba daya” Ya kara da cewa, ba a la’akari da wanene kaba jinin musulmi ne,ko ba musulmi ba,in dai sunan sa  rai, za a bas hi jinni domin ya rayu, idan yaso shi ya yanke ma kansa hukuncin zabin abin da zaya yi.
Malam Yakubu ya tabbatar da cewa, bayar da jinni yana kara lafiyar mutum,sannan kuma ta hanyar bayarwar za a iya fahimtar yanayin lafiyar mutum ta yadda idan mutum yana da wata matsala, za a iya shawo kanta cikin sauri ba tare da ta ketara zuwa ga wani ba.’ka gay a sami lada kuma ya san matsayin lafiyarsa’ daga nan sai malam Yakubu ya karfafa sadaukar da jinin da cewa, ba sai lokacin Ashura ba ne kadai  za a iya bayarwa, a’a  akwai bukatar mutum ya bayar idan akwai bukata matukar dai  za a iya yin hakan.Sai ya yi fatan ganin Allah  ya kai mu lokacin da zamu bayar da rayuwar mu gaba daya domin daukar fansar zaluncin da aka yi ma Imam Husain(AS).
Likitan da yake jagorantar kungiyar karbar jinin da rabashi ga mabukata a wannan aikin, Dakta Iisma’il Buhari, kira ya yi ga jama’a da suke dari-darin bayar da gudunmuwar jini da cewa, bayarwar ba bata da wata matsala, domin ba haka nan ake dibar jinin mutum ba har sai an gabatar da tambayoyin da za su kai ga fahintar cewa, za a iya dibar jinin mutum lafiya lau ba tare da ya sami wata matsala ba, idan kuwa aka fahinci cewa, dibar zata haifar masa da matsala, to bama za a diba ba.
Sai ya nemi sauran jama’a  da a daure a rika bayarwa, domin bayarwar abu ne mai muhimmanci, saboda ceton rayuwa. Ya kara da cewa, ‘abin lura shi ne, idan jama’a basu bayar da wannan gudunmuwa ba, to babu inda za a je a samo shi.” Sai ya tabbatar da cewa,bayarwar ba matsala ba ce sai ma lafiya ta za a kara samu. ‘kodai mutum ya bayar, ko bai bayarba, jinin yakan  lalace a cikin kowane wata  Allah ya sake samar da wani’Sai ya yaba ma ‘yanuwa musulmi da suke  kokarin tallafawa da jinin kyauta ba tare da ana biyansu  kudi ba.
Malam Abdul karim Usamatu, shi ne wanda yake jagorantar kwamitin  ISMA  a wannan yanki, ya  bayyana karuwar jama’a da suke bayar da wannan gudunmu da cewa, ‘ fahimtar muhimmanci bayarwar ne  da jama’a suke yi sakamakon bayanin da kwamitin yake yi lokaci-lokaci musamman lura da suke yi cewa, bayar da jinin ibada ne sannan kuma yana kara lafiya ne ga duk wanda ya bayar.
A bana dai adadin wadanda zasu  bayar da jinin ya nunka na bara idan aka lura da al’kalumman da kwamitin kiwon lafiya  na harkar musulunci (ISMA) ya tattara a wannan shekara.  

'YANUWA SUN BAYAR DA GUDUNMWAR JINI A KATSINA


Sadaukar da jini don bayarwa ga masu bukatarsa a irin wannan lokaci na nuna juyayin Ashura kamar zaburantarwa ne a gare mu, dokmin Imam Husaini (AS)ba jininsa kawai ya sadaukar ba, yama sadaukar da rayuwarsa ne gaba daya data iyalansa dama Sahabbansa.Malam Yakubu Yahaya  wakilin ‘yanuwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky(H) na katsina ya b ayyana haka a lokacin da yake tattaunawa da wakilinmu a yayin bayar da jini da ‘yanuwan suka yi albarkacin sadaukarwar Imam Husaini(AS).  
Malam Yakubu yahaya ya bayyana cewa, “an san muhimmancin bayar da jini a wannan zamani, domin shi jini jigo ne a rayuwa, shi yasa ma zaka ga  ana farautar jini harma da kudi domin mutane su  samu su rayu, musamman yayin bukata, ko saboda haihuwa, hadari da makamantansu. Shi ya sanya masana suka muhimmantar da bayar das hi.”Sai ya karfafa bukatar bayar da jini muddin hakan zaya amfanar da dan Adam.
Ta fuskacin addini, malam Yakubu ya bayyana cewa, idan mutum ya bayar da jini aka ceto rayuwar mutum daya, ladar da zaya samu kamar ya ceto rayuwar al’umma ne baki daya.Ya karfafa maganar da ayar nan dake nuni da cewa, ‘wanda ya  kasha rai, kamar ya kasha rayuka ne baki daya, wanda ya raya rai daya, ,kamar ya raya rayuka ne gaba daya” Ya kara da cewa, ba a la’akari da wanene kaba jinin musulmi ne,ko ba musulmi ba,in dai sunan sa  rai, za a bas hi jinni domin ya rayu, idan yaso shi ya yanke ma kansa hukuncin zabin abin da zaya yi.
Malam Yakubu ya tabbatar da cewa, bayar da jinni yana kara lafiyar mutum,sannan kuma ta hanyar bayarwar za a iya fahimtar yanayin lafiyar mutum ta yadda idan mutum yana da wata matsala, za a iya shawo kanta cikin sauri ba tare da ta ketara zuwa ga wani ba.’ka gay a sami lada kuma ya san matsayin lafiyarsa’ daga nan sai malam Yakubu ya karfafa sadaukar da jinin da cewa, ba sai lokacin Ashura ba ne kadai  za a iya bayarwa, a’a  akwai bukatar mutum ya bayar idan akwai bukata matukar dai  za a iya yin hakan.Sai ya yi fatan ganin Allah  ya kai mu lokacin da zamu bayar da rayuwar mu gaba daya domin daukar fansar zaluncin da aka yi ma Imam Husain(AS).
Likitan da yake jagorantar kungiyar karbar jinin da rabashi ga mabukata a wannan aikin, Dakta Iisma’il Buhari, kira ya yi ga jama’a da suke dari-darin bayar da gudunmuwar jini da cewa, bayarwar ba bata da wata matsala, domin ba haka nan ake dibar jinin mutum ba har sai an gabatar da tambayoyin da za su kai ga fahintar cewa, za a iya dibar jinin mutum lafiya lau ba tare da ya sami wata matsala ba, idan kuwa aka fahinci cewa, dibar zata haifar masa da matsala, to bama za a diba ba.
Sai ya nemi sauran jama’a  da a daure a rika bayarwa, domin bayarwar abu ne mai muhimmanci, saboda ceton rayuwa. Ya kara da cewa, ‘abin lura shi ne, idan jama’a basu bayar da wannan gudunmuwa ba, to babu inda za a je a samo shi.” Sai ya tabbatar da cewa,bayarwar ba matsala ba ce sai ma lafiya ta za a kara samu. ‘kodai mutum ya bayar, ko bai bayarba, jinin yakan  lalace a cikin kowane wata  Allah ya sake samar da wani’Sai ya yaba ma ‘yanuwa musulmi da suke  kokarin tallafawa da jinin kyauta ba tare da ana biyansu  kudi ba.
Malam Abdul karim Usamatu, shi ne wanda yake jagorantar kwamitin  ISMA  a wannan yanki, ya  bayyana karuwar jama’a da suke bayar da wannan gudunmu da cewa, ‘ fahimtar muhimmanci bayarwar ne  da jama’a suke yi sakamakon bayanin da kwamitin yake yi lokaci-lokaci musamman lura da suke yi cewa, bayar da jinin ibada ne sannan kuma yana kara lafiya ne ga duk wanda ya bayar.
A bana dai adadin wadanda zasu  bayar da jinin ya nunka na bara idan aka lura da al’kalumman da kwamitin kiwon lafiya  na harkar musulunci (ISMA) ya tattara a wannan shekara.  

Friday, November 15, 2013

AN GABATAR DA MUZAHAHARAR ASHURA A KATSINA



 Tun da sanyin safiyar wannan rana ta Alhamis ne ta 11/1/1435 hijiriyya, dubun dubatar al’ummar musulmi suka fara yi ma garin Katsina kabbara domin amsa kiran Sheikh Ibrahim Almagri(H) na gabatar da muzaharar Ashura don nuna jaje ga Manzon Allah da Iyalansa na kisan da  rundunar yazidu (L) ta yi ma Imam Husaini(AS) da sauran zuriyar Annabi(S) da kuma nSahabban Imam Husainin a karbala.
malam Yakubu ya mika ta’aziyyar ‘yanuwa  da suka halarci wannan muzahara ga Manzon Allah da iyalansa masu tsarki, sannan ya kuma mika wannan ta’aziyya ga jagororin gwagwarmayar duni a wannan lokaci haka kuma zuwa ga sheikh zakzaky(H). Daga nan ya bayyana  cewa,wannan abu da ya faru ga  iyalan Annabi(S) kiyayya ce ,inda ya tabo irin yadda Kuraishawa suka shiga musulunci akan dole bayan da suka ga an rinjaye su.”Suun shiga musulunci ne ganin babu yadda zasu  yi domin an rinjaye su, sai suka ga bari su shiga cikinsa  domin su bata addsinin” kawo maganar Abu- jahal da ya ce, ba suna tuhumar Muhammadu ba ne da wani aibu.Sai malam Yakubu y ace, watsi da wasicin manzon Allah ne da ya yi a Gadir da   aka yi , shi ne ya jawo hawan Yazidu dan Mu’awiyya mulkihar ya yi aika-aikar da aka yi.
Malam yakubu ya kara da cewa, bayan wannan kisan ne da suka yi ,sai aka yi kokarin kawo ruwayoyi da suke nuna matsayin wannan rana ta ashura domin rufe wannan aibu, ya ci gaba da cewa, an yi kokarin shafa ma wadannan mabarnata farin fenti aka wanke su aka ce ma su ne masu addinin gaskiya.sai y ace, wadannan karairayi duk na banu Umayya ne don su rufe laifin da suka yi ma Allah da manzo.Sai y ace, wannan abiun da muke yi ba wasa bane ba kuma yayi ba nedomin l;olkacin yayi ya wuce a wajen mu, saboda tun muna yi mu kadai har gas hi yanzu muna yi tare da jikokinmu,ddon haka addini muke ba wasa ba.

Wednesday, November 13, 2013

TA'AZIYYAR MALAM YAKUBU YAHAYA KATSINA GA SHEMA

 
Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa musulmi almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky(H) na da’irar Katsina, ya kai ziyarar ta’aziyya ga gwamnan Jihar ta katsina Alhaji Ibrahim Shehu Shema sakamakon rasuwa da  mahaifin gwamnan ya yi a ranar Litinin 11//11/2013 da ta gabata.


Malam yakubu ya jajanta ma gwamnan da zuriyar sa akan wannan rashi na mahaifinsu. Malam yakubu ya bayyana ma gwamnan muhimmancin yin addu’a ga mamacin inda ya sheda masa bukatuwa da mamata suke da ita ta addu’a da kuma hakkin day a rataya ga wuyan   ‘ya’ya na yin addu’a ga iyaye.
Gwamnan na Katsina Alhaji Ibrahim Shema ya gode ma Malam yakubun dangane da wannan ta’aziyya  day a kai masu, sannan ya yi rokon isar da godiyarsa ga Sheikh Ibarahim Zakzaky(H) saboda wannan karamci da aka yi masu.
Wasu daga cikin ‘yanuwa ne dai suka raka Malam yakubu  wannan  ta’aziyya.

SANARWA TA MUSAMMAN

Sashen da yake kula da wallafa labaran harka a wannan dandali, yana bayar da hakuri ga dimbin masu karatu da suka dogara ga wannan shafi don samun labaran harkar musulunci a wannan nahiya,rashin samun labarai daga wannan zaure ya faru ne saboda wasu matsaloli,amma yanzu da yardar Allah mun dan shawo kansu. 
Da fatan za aci gaba da yi mana addu'a.