Sunday, July 8, 2012

AN GABATAR DA BIKIN YAUMUT TAKLIF A GARIN KATISANA

An bayyana takalifi da cewa shi ne a sa ka yin abinda baka son yi, a kuma hana ka yin abinda kake son ka yi. Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) na da’irar Katisna da kewaye ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi ga kananan yara maza da matan da suka kai shekarun wajabcin shari’a a kansu, a bukin “yaumut taklif” wanda dandalin matasa na yankin ya shirya aka gabatar da shi a ranar Lahadi 19/ 8/1433 a markazin ‘yanuwan dake garin Katsina.
A farkon jawabin sai da Malam Yakubu ya kawo ma yaran wasu abubuwa da yara suka fi fifitawa, inda ya tambaye su abin da yaro ya fi bukata tsakanin ranaikun karatu da kuma na hutun makaranta, ranar barci da tashi ayi salla cikin lokaci dangane da sallar Asubahi da dai sauran misalai makamantan wadannan. Sai ya kara bayanin cewa, shi takalifi baya nufin Allah ya dankara ma mutum aiki ne, sai dai domin a lahira Allah za ya canja ma mutum din ne da abin da ya hanu a duniya da abinda yake a lahira.
Malam Yakubu ya bayyana ma yaran cewa, ana fara addini ne tun mutum yana yaro, ba sai an girma ba ne ake fara yinsa, sai ya ce, idan ka ga tsohon banza, to babu shakka yaron banza ya taso, haka ma abin yake idan ka ga tsohon kirki, to ya taso ne a yaron kirki, inda ya ba yaran misalin Shehu Usman dan Fodiyo muijaddadi (RA) yadda ya taso da kirki tun yana yaro ya kuma yi rayuwar kirki, ga kuma Imam Khomaini(KS) shi ma haka ya taso, kana Sayyid Zakzaky(H) shi ma haka rayuwarsa take, sai ya karfafa cewa, duk inda ka ga yaron kirki to za ya zama tsohon kirki, haka ma idan kaga sabanin wannan. Sai ya tambayi yaran ko akwai wanda ya ke so ya yi irin tsufan su Malam Zakzay (H), inda duk cikar su suka amsa da cewa, E!. Sai ya yi fatan Allah (T) ya tabbatar da haka.
Malam Yakubu, ya jawo hankulan yaran da cewa, idan aka kai shekaru irin nasu, to ba a bukatar yaro ya bata Sallarsa idan yana yi, ko kuma ya boye ya ci wani abu idan yana Azumi, ya ce , wanda duk ya yi haka ,to ana binsa bashi sai ya rama su, idan ma azumi ne sai ya kara da guda sittin(kaffara) sakamakon bata daya da ya yi. Sannan ya kiraye su da cewa, ba a bukatar su zama masu karya , cin amana, su kuma zamo masu biyayya ga iyayensu, su kuima lizimci yin amfani da abubuwan da suke koyo a makarantu na addini da aikatawa tun daga wannan rana har zuwa mutuwa. Sannan ya bukaci malamai da iyaye da su kara kulawa da sallar yaran a makarantu da kuma gidajensu har ya zamo sun saba. Sannan aka gabatar da salla raka’a biyu wadda Malam Yakubun ya jagoranta domin koya ma yaran yadda ake bukatar su rika gabatar da ita a duk sa’adda lokacin ta ya gabato.
Shi dai wannan biki na ‘yaumut taklifi’ an gabatar da shi ne da zimmar zaburantar da yaran da shekarunsu suka kama daga tara zuwa sama ga ‘yan mata, su kuma maza daga goma sha biyar .
Saidai a wanna karo an lura da cewa, wadanda suka halarci wannan taro akwai kananan yaran da shekarun nasu basu kai wadanda aka bukata ba, abinda ya jawu yin kira da cewa, wasu sai an sake dawowa da su a wasu shekaru masu zuwa nan gaba, kamar yadda Malam Yakubu ya bukata. An dai kammala wannan biki karo na farko cikin nasara.

No comments:

Post a Comment