“Imam Husain(AS) ya yi shahada ne tun
bayan wafatin manzon Allah(S), dole ne mu tunatar da junan mu wannan, idan bamu
fahimci haka ba, ba zamu fahimci abinda ya faru a Karbala ba” Malam Yakubu
Yahaya wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Zakzaky(H) ne ya bayyana haka a yayin
rufe Muzahahar nuna jaje da alhini ga Manzon Allah da Iyalaansa masu tsarki da aka
gabatar a ranar Lahadi 11/1/1434 sakamakon kisan gillar da makiyan Allah
suka yi ma Imam Husaini dan Ali dan Abi Dalib(AS) a ranar goma ga Muharram da
aka fi sani da ranart Ashura.
A yayin da yake rufe muzaharar, malam
Yakubu wanda shi ne ya jagoranci
muzaharar har zuwa karasa ta, ya fara ne da mika ta’aziyya ga
Manzon Allah wanda ya ce,”muke da yakinin yana tare da mu,
sannan ga Sayyida Zahara, Imam Ali (AS) da sauran
Iyalan gidan Manzon Allah tsarkaka har ya zuwa ga Imamul Asr (AJ), sannan ya mikata ga Sayyid Zakzaky (H), Sayyid
khamina’I da Sayyid Nasrullah da sauran ‘yantattaun bayin Allah. Sai ya jawo hankalin al’ummar musulmi
da cewa, dole mu tunatar da juna wannan dominb idan ba a fahimci wannan ba,
ba za a ma fahimci abinda ya faru a
Karbala’I din ba.sannan ya cxe, kafin ManzonAllah ya bar duniya, ya ayyana
yadda dduniya zata zauna daidai, amma wadansu manzya suka fadi jarabawa kamarf
yadda kowa zaya iya faduwa jarabawa saboda halayya irin ta dan Adam, haka suka
fadi jarabawa ta hanyar canja wasiyyar da Manzon Allah ya yi ta wanda za a bi
bayan wafatinsa. Ya ce, “Manzo ya ce, ku yi biyayya ga Imam Ali(AS) da yin
jihadi da saurarensa, sai suka canja
bayuan wafatin,suka yi, jihadin sukja koyar da karatau da yada addini, amma ba
bayan wanda Manzo ya ce ba, a karshe ma suka kashe Imam Alin, haka kuma suka kashe
Imam Hasan sannan wanda ya gada daga
baya ya kashe Imam Husaini (AS). Ya kara da cewa, bayan kauce ma waccan wasiyya
ce, Imam Husaini ya fita domin kawo gyara,kuma wannan shi ne sanadiyyar kashe
shi kisan wulakanci Kisa irin na rashin
mutunci. Ya yi nuni da cewa, wadanda suka kashe Imam Husaini muslmi ne wadanda
suka sauya daga turbar da Manzon Allah ya shata suka yi wani abu daban kuma
wannan shi ne ya kai mu halin da muke ciki a halin yanzu.Malam Yakubu nya tabo
irin yadda aka wulakanta jikokin Manzon Allah
a wannan fili na Karbala cikin yanayi na
tursasawa da kishirwantarwa domin an hana su ko ruwa ma su kurba, sannan
bayan an karkashe su aka iza kiyarsu gaba ana wulakanta su, cin mutunci ta
tozartawa. Ya ce, duk wadannan abubuwa suna nan cikin littattafan tarihi a
rubuce, kjuma wannan wai shi ne sunna.Sannan y ace Allah ya yi mana baiwa da
wanda ya haska mana , ya fahimtar da mu yadda abin yake. “dadewa akan ba daidai
ba, baya mayar da abin daidai, a komo kan daidai” in ji shi.
Malam Yakubu ya ce, Allahya so ya kuma
ga dammar maido da addini kamar yadda ya ce” domin ya bayyanar da addini akan
dukkan addinai ko da kafirai sun ki” to lokacin yin hakan ya yi.Sannan y ace
waki’ar Karbala bayan shekartu dbu da kimanin dari kusan hudu, yanzu ta motsa
zukata, ta kuma nuna cewa, lallai irin abin da Imam Husaini ya yi, shi ne ya
kamata al’umma ta yi domin kwatar kai daga
zalunci.
Sai ya yi kira ga musulmi su dawo kan
saiti , madamar ba a saita ba, to za ayi ta tafiya akan addinin da Mu’awiyya ya
gina wasu suka zo suka gadsa ake ce masaa sunna wal jama’a, sai ya ce “dole
tunani ya canza.”
Ya nuna takaicin yadda malamai suka koma
kayan aikin hukumomi sakamakon irin wannan koyarwa ta Umayyawa.Ya nuna yadda
ake rayuwa a wannan kasa, inda yace da akwai gara,da sai ace4 gara kafircin
Yazidu da na wannan kasa, domin shi kafircin Yazidu an yi masa rumfa ne da
cewa, musulunci har ma an ace ma Yazidun sarkin Musulmi, amma shi mkafircin
Nigeriya bai yarda da Qur’ani ba, bai yarda a buda Qur’anin ba ace Allah ya ce
ba.Don haka akwai matsala babba inji Malamin.Ya kara da cewa, a loikacin Yazidu
ana zuwa jihadi, amma na wannan kasa, dan musulmi ne zaya buda bakinsa ya ce babu
ruwansa da addini.”don haka kafirci ake
yi a wannan kasa, mahukuntan wannan kasa kafirci suke jagoranta, kuma wanda duk
ya mutu yana biyayya ga kafirci, zaya karba tambayta gaban Allah (T) kujma baya
da amsa, saannan kada murtum ya dauka da saauki, babu sauki.
Sai ya kamala da cewa, “abinda yasa mu
ka dauki wannan hanya, shi ne domin mun yanke kauna akan gyaruwar wanna kasa, shi yasa muka zabi hanyar komawa
lahira, kuma zamu iya tunkarear kowace hanyar zuwa lahira, idan akwai ja ,ko
baka ko fara ko dorowa, to shirye muke mu tunkare ta, saboda mun riga mun yanke
shawara, dam nu yi asarar lahira, gara mu yi asarar duniya, idan ma zamu ga wanda yake so ya aika
mu lahirar, muna maraba da shi, wannan shi ne abinda shugabanmu Sayyid
Zakzaky(H) yak e ce mana, idan muka ga inda ake bude wuta , mu sa kai wajen”Sannan
y ace wannan shi ne mafitarmu, idan Allah ya ga dama ya wanzar mana da addini,
mu bauta ma Allah, idan kuma yagta dama ya yi mana irin na Imam Husaini, to mu
bamu kai sharer takalmin Imam din ba, amma maganar biyayya ga kafircin waannan
kasa na dad a na yanzu , ba bu domin dai sun riga sun yi asarar mu da duk
zuriyarmu,”
Muzaharar wadda aka kwashe kimanin awa
uku da rabi ana gabatar da ita ta kewaye manyan titunan birnin Katsina cikin
natsuwar da take dauke da sakon nuna juyayi akan cin mutuncin da aka yi ma
Manzon Allah a bayan wafatinsa, kusan dukkan wadanda suke a sahun muzahgarar
suna tafe ne suna rera wakokin jaje wasuma suna tafe ne suna zubar da hawaye na
nuna alhinin musibar da ta sauka ma iyalan Annabin Rahama(S) a wannan ranar ta
Ashura.
Al’ummar garin Katsina dfa dama sun
taya ‘yanuwa wannan juyayi, a lokacin da ake aiwatar da ita wannan
muzahara.