A ranar Talatar da ta gabata ne, aka kawo karshen zaman makokin Shahadar Imam Husaini(AS) wanda Da’irar ‘yanuwa almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) taKatsina ta shirya kuma wakilin ‘yanuwan Da’irar ta Katsina Malam Yakubu Yahaya ya kwashe kimanin kwana ashirin yana gabatarwa.
A wannan karatu na zaman makokin Imam Husaini(AS), Malam Yakubu ya kawo Dalilai da suka jawo wannan waki’a ta ashura, inda ya karanto daga cikin littattafan Ahlussunati, abubuwan da suka faru tun daga lokacin da Manzon Allah ya riski Rahamar Mahaliccinsa, inda ya karanto abubuwan da suka shafi warware bai’a ta hanyar canza nadi tare da zaben halifanci sabanin wanda Manzon Allah ya yi.
Bayan karantar yadda waki’ar ta Ashura ta faru, an kuma karanto abubuwa marasa dadin ji da addini ya gamu da su bayan kisan gillar da aka yi ma Imam Husaini(AS) kamar kisan Sahabbai da ruguza garin Madinar Manzon, yakar Makka tare da rusa Ka’aba ta hanyar jifar ta da majaujawa da rundunar Yazidu ta yi.
Bayan kammala karatun ne , aka yi addu’ar neman samun damar daukar fansar wannan ta’addanci da makiya Allah suka yi wai kuma da sunan su Musulmi ne. Sannan malam Yakubun ya yi kira ga musulmi da su karanci wannan addini na musulunci ta hakikanin koyarwar gidan Annabi, tun da dai wannan addinin Annabi Muhammad ne aka aiko da shi, kuma koyarwarsa tana nan tare da Iyalan gidansa.
A wannan karatu na zaman makokin Imam Husaini(AS), Malam Yakubu ya kawo Dalilai da suka jawo wannan waki’a ta ashura, inda ya karanto daga cikin littattafan Ahlussunati, abubuwan da suka faru tun daga lokacin da Manzon Allah ya riski Rahamar Mahaliccinsa, inda ya karanto abubuwan da suka shafi warware bai’a ta hanyar canza nadi tare da zaben halifanci sabanin wanda Manzon Allah ya yi.
Bayan karantar yadda waki’ar ta Ashura ta faru, an kuma karanto abubuwa marasa dadin ji da addini ya gamu da su bayan kisan gillar da aka yi ma Imam Husaini(AS) kamar kisan Sahabbai da ruguza garin Madinar Manzon, yakar Makka tare da rusa Ka’aba ta hanyar jifar ta da majaujawa da rundunar Yazidu ta yi.
Bayan kammala karatun ne , aka yi addu’ar neman samun damar daukar fansar wannan ta’addanci da makiya Allah suka yi wai kuma da sunan su Musulmi ne. Sannan malam Yakubun ya yi kira ga musulmi da su karanci wannan addini na musulunci ta hakikanin koyarwar gidan Annabi, tun da dai wannan addinin Annabi Muhammad ne aka aiko da shi, kuma koyarwarsa tana nan tare da Iyalan gidansa.
No comments:
Post a Comment