Monday, November 26, 2012

MUZAHARAR ASHURA A KATSINA TA KAYATAR


“Imam Husain(AS) ya yi shahada ne tun bayan wafatin manzon Allah(S), dole ne mu tunatar da junan mu wannan, idan bamu fahimci haka ba, ba zamu fahimci abinda ya faru a Karbala ba” Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Zakzaky(H) ne ya bayyana haka a yayin rufe Muzahahar nuna jaje da alhini ga Manzon Allah da Iyalaansa masu tsarki   da aka  gabatar a ranar Lahadi 11/1/1434 sakamakon kisan gillar da makiyan Allah suka yi ma Imam Husaini dan Ali dan Abi Dalib(AS) a ranar goma ga Muharram da aka fi sani da ranart Ashura.
A yayin da yake rufe muzaharar, malam Yakubu wanda shi ne  ya jagoranci muzaharar har zuwa karasa ta, ya fara ne da  mika ta’aziyya ga
Manzon Allah wanda   ya ce,”muke da yakinin yana tare da mu, sannan  ga  Sayyida Zahara, Imam Ali (AS) da sauran Iyalan gidan Manzon Allah tsarkaka har ya zuwa ga Imamul Asr (AJ), sannan  ya mikata ga Sayyid Zakzaky (H), Sayyid khamina’I da Sayyid Nasrullah  da  sauran ‘yantattaun bayin  Allah. Sai ya jawo hankalin al’ummar musulmi da cewa, dole mu tunatar da juna wannan dominb idan ba a fahimci wannan ba, ba  za a ma fahimci abinda ya faru a Karbala’I din ba.sannan ya cxe, kafin ManzonAllah ya bar duniya, ya ayyana yadda dduniya zata zauna daidai, amma wadansu manzya suka fadi jarabawa kamarf yadda kowa zaya iya faduwa jarabawa saboda halayya irin ta dan Adam, haka suka fadi jarabawa ta hanyar canja wasiyyar da Manzon Allah ya yi ta wanda za a bi bayan wafatinsa. Ya ce, “Manzo ya ce, ku yi biyayya ga Imam Ali(AS) da yin jihadi da saurarensa, sai  suka canja bayuan wafatin,suka yi, jihadin sukja koyar da karatau da yada addini, amma ba bayan wanda Manzo ya ce ba, a karshe ma suka kashe Imam Alin, haka kuma suka kashe  Imam Hasan sannan wanda ya gada daga baya ya kashe Imam Husaini (AS). Ya kara da cewa, bayan kauce ma waccan wasiyya ce, Imam Husaini ya fita domin kawo gyara,kuma wannan shi ne sanadiyyar kashe shi  kisan wulakanci Kisa irin na rashin mutunci. Ya yi nuni da cewa, wadanda suka kashe Imam Husaini muslmi ne wadanda suka sauya daga turbar da Manzon Allah ya shata suka yi wani abu daban kuma wannan shi ne ya kai mu halin da muke ciki a halin yanzu.Malam Yakubu nya tabo irin yadda aka wulakanta jikokin Manzon Allah  a wannan fili na Karbala cikin yanayi na  tursasawa da kishirwantarwa domin an hana su ko ruwa ma su kurba, sannan bayan an karkashe su aka iza kiyarsu gaba ana wulakanta su, cin mutunci ta tozartawa. Ya ce, duk wadannan abubuwa suna nan cikin littattafan tarihi a rubuce, kjuma wannan wai shi ne sunna.Sannan y ace Allah ya yi mana baiwa da wanda ya haska mana , ya fahimtar da mu yadda abin yake. “dadewa akan ba daidai ba, baya mayar da abin daidai, a komo kan daidai” in ji shi.
Malam Yakubu ya ce, Allahya so ya kuma ga dammar maido da addini kamar yadda ya ce” domin ya bayyanar da addini akan dukkan addinai ko da kafirai sun ki” to lokacin yin hakan ya yi.Sannan y ace waki’ar Karbala bayan shekartu dbu da kimanin dari kusan hudu, yanzu ta motsa zukata, ta kuma nuna cewa, lallai irin abin da Imam Husaini ya yi, shi ne ya kamata al’umma ta yi domin kwatar kai daga  zalunci.
Sai ya yi kira ga musulmi su dawo kan saiti , madamar ba a saita ba, to za ayi ta tafiya akan addinin da Mu’awiyya ya gina wasu suka zo suka gadsa ake ce masaa sunna wal jama’a, sai ya ce “dole tunani ya canza.”
Ya nuna takaicin yadda malamai suka koma kayan aikin hukumomi sakamakon irin wannan koyarwa ta Umayyawa.Ya nuna yadda ake rayuwa a wannan kasa, inda yace da akwai gara,da sai ace4 gara kafircin Yazidu da na wannan kasa, domin shi kafircin Yazidu an yi masa rumfa ne da cewa, musulunci har ma an ace ma Yazidun sarkin Musulmi, amma shi mkafircin Nigeriya bai yarda da Qur’ani ba, bai yarda a buda Qur’anin ba ace Allah ya ce ba.Don haka akwai matsala babba inji Malamin.Ya kara da cewa, a loikacin Yazidu ana zuwa jihadi, amma na wannan kasa, dan musulmi ne zaya buda bakinsa ya ce babu ruwansa da addini.”don haka kafirci  ake yi a wannan kasa, mahukuntan wannan kasa kafirci suke jagoranta, kuma wanda duk ya mutu yana biyayya ga kafirci, zaya karba tambayta gaban Allah (T) kujma baya da amsa, saannan kada murtum ya dauka da saauki, babu sauki.
Sai ya kamala da cewa, “abinda yasa mu ka dauki wannan hanya, shi ne domin mun yanke kauna akan gyaruwar wanna  kasa, shi yasa muka zabi hanyar komawa lahira, kuma zamu iya tunkarear kowace hanyar zuwa lahira, idan akwai ja ,ko baka ko fara ko dorowa, to shirye muke mu tunkare ta, saboda mun riga mun yanke shawara, dam nu yi asarar lahira, gara mu yi asarar  duniya, idan ma zamu ga wanda yake so ya aika mu lahirar, muna maraba da shi, wannan shi ne abinda shugabanmu Sayyid Zakzaky(H) yak e ce mana, idan muka ga inda ake bude wuta , mu sa kai wajen”Sannan y ace wannan shi ne mafitarmu, idan Allah ya ga dama ya wanzar mana da addini, mu bauta ma Allah, idan kuma yagta dama ya yi mana irin na Imam Husaini, to mu bamu kai sharer takalmin Imam din ba, amma maganar biyayya ga kafircin waannan kasa na dad a na yanzu , ba bu domin dai sun riga sun yi asarar mu da duk zuriyarmu,”
Muzaharar wadda aka kwashe kimanin awa uku da rabi ana gabatar da ita ta kewaye manyan titunan birnin Katsina cikin natsuwar da take dauke da sakon nuna juyayi akan cin mutuncin da aka yi ma Manzon Allah a bayan wafatinsa, kusan dukkan wadanda suke a sahun muzahgarar suna tafe ne suna rera wakokin jaje wasuma suna tafe ne suna zubar da hawaye na nuna alhinin musibar da ta sauka ma iyalan Annabin Rahama(S) a wannan ranar ta Ashura.
Al’ummar garin Katsina  dfa dama sun  taya ‘yanuwa wannan juyayi, a lokacin da ake aiwatar da ita wannan muzahara.


No comments:

Post a Comment