MANUFAR BUDE WANNAN DANDALI NA MEDIAFORUM KATSINA, SHINE YADA HARKOKIN KIRAN DA MAULANA SAYYID IBRAHIM ZAKZAKY(H)YAKE YI NE.TARE DA KAWO LABARAN ABUBUWAN DA KE FARUWA NA WANNAN HARKAR TA MUSULUNCI A WANNAN YANKI NA KATSINA DAMA WASU YANKUNA, NA YUNKURIN WAYAR MA AL'UMMA KAI DANGANE DA AL'AMARIN MUSULUNCI, MUSAMMAN ABINDA YA SHAFI KOYARWAR AHLUL-BAITIN MANZON ALLAH(AS).
Friday, August 20, 2010
TUKIYYA TANA NAN A AL’QUR’ANI DA HADISAN MANZON ALLAH
Tare da Malam Yakubu Yahaya Katsina
DAGA: ABDUL AZIZI
An karyata tuhumar da ake yi ma mabiya Ahlul-Bayt (A.S) na cewar su munafukai ne ko suna fadar abin da ba haka yake ba a cikin zukatansu. saboda wai suna yin tukiyya ne. Malam yakubu Yahaya ya yi wannan karyatawa a lokacin da yake Karin bayani akan fassarar ayar nan da Allah madaukakin Sarki yake bayanin cewa” muminai kada su riki kafirai majibinta al’amurransu koma bayan Muminai, wanda duk ya aikata haka, shi ba bakin komai yake ba a wurin Allah, sai in kun ji tsoro da ‘yar kariya ( watau tukiyya) , Allah yana maku kashedin kansa, kuma makoma a wajen Allah take” ya kara da cewa, irin wannan Magana jahiltar al’Qur’ni ne domin wannan al’amari na Tukiyya karar yake a cikin littafin Allah.
Ya ce Ma’anar tukiyya shine Mutum ya kare kansa daga wani wanda zaya cutar da rayuwarsa ko dukiyarsa ko mutuncinsa, kuma ana yin ta ne domin kare addini” kana hanya ta addini , kana kira zuwa ga Allah, amma ga wani zai takura maka ko zai raba ka da rayuwarka ko dukiyarka ko ya cutar da kai sai dai kace Allah ya isa, ka samu ka yi Tukiyya anan , ka nuna kamar ka bari, amma a zuciyarka ba da gaske ba ne, kuma da ka sami dama kana ci gaba da abubuwanka” Ya yi bayanin cewa an samu wannan ne daga abinda ya faru ga babban Sahabin Annabi(S.A.W) Ammar bn Yasir a lokacin da Mushirikai suka rika azabtar da shi gami da mahaifansa Yasir da Sumayya abin da ya yi sanadiyyar shahadar mahaifan nasa, shi kuma Ammar ya kasa daurewa da irin wannan azaba har sai da ya yi maganganu marasa kyau ga Annabi sannan suka rabu da shi.
Da ya koma wurin manzon Allah tsirar Allah ta tabbabata gare shi da Iyalan gidansa yana kuka, da Manzo ya tambaye shi cewa, ya ya yake ji? Ammar ya tabbatar da cewa daram yake ji a zuciyarsa. Sai Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi da Iyalan gidansa ya ce,” Ammar yana cike da Imani tun daga kwakwalwar kansa har zuwa akaifar kafarsa, idan gobe suka kara yi maka irin wannan ka kara yi masu”. Wannan ya sa Allah (T) ya saukar da aya “ sai wanda aka tursasa shi, alhali zuciyarsa na cike da Imani”
Malam Yakubu ya kuma karanto Hadisai na Annabi a ruwayoyin Ahlulsunna da dama, da suka nuna ana yin Tukiyyah idan bukatar yin nata ta taso. sannan ya ce ya kamata a kara bincikawa domin a fahinci yadda al’amarin yake. Sannan ya ce, wannan batu na Tukiyya ya samo asali ne tun a farkon Musulunci, ba ‘yan Shi’a ba ne suka kirkiro, amma su suka fi yinta sabo da halin da suka sami kansu na takura da fafara da ake yi masu alokacin mulkin Umayyawa da Abbasiyawa, sai ya zamo sune suka fi bukatuwa zuwa ga yinta. Su kuwa Sunna basu shahara da yinta ba saboda basu da matsala da mahukunta, bilhasilima sune suke bayar da fatawa ga mahukuntan.” Wannan ya isa hujja ga mai neman gaskiya “
Malam Yakubu ya kara karanto wasu ruwayoyi da suka nuna yadda Sahabban Manzon Allah suka rika yin ta bayan rasuwar manzon Allah saboda abubuwan da suka biyo bayan rasuwar ta Annabin. Sai ya bayyana bukatar Musulmi su kara karantar Musuluncin domin kauce ma shiga cikin hadari.
DAGA: ABDUL AZIZI
An karyata tuhumar da ake yi ma mabiya Ahlul-Bayt (A.S) na cewar su munafukai ne ko suna fadar abin da ba haka yake ba a cikin zukatansu. saboda wai suna yin tukiyya ne. Malam yakubu Yahaya ya yi wannan karyatawa a lokacin da yake Karin bayani akan fassarar ayar nan da Allah madaukakin Sarki yake bayanin cewa” muminai kada su riki kafirai majibinta al’amurransu koma bayan Muminai, wanda duk ya aikata haka, shi ba bakin komai yake ba a wurin Allah, sai in kun ji tsoro da ‘yar kariya ( watau tukiyya) , Allah yana maku kashedin kansa, kuma makoma a wajen Allah take” ya kara da cewa, irin wannan Magana jahiltar al’Qur’ni ne domin wannan al’amari na Tukiyya karar yake a cikin littafin Allah.
Ya ce Ma’anar tukiyya shine Mutum ya kare kansa daga wani wanda zaya cutar da rayuwarsa ko dukiyarsa ko mutuncinsa, kuma ana yin ta ne domin kare addini” kana hanya ta addini , kana kira zuwa ga Allah, amma ga wani zai takura maka ko zai raba ka da rayuwarka ko dukiyarka ko ya cutar da kai sai dai kace Allah ya isa, ka samu ka yi Tukiyya anan , ka nuna kamar ka bari, amma a zuciyarka ba da gaske ba ne, kuma da ka sami dama kana ci gaba da abubuwanka” Ya yi bayanin cewa an samu wannan ne daga abinda ya faru ga babban Sahabin Annabi(S.A.W) Ammar bn Yasir a lokacin da Mushirikai suka rika azabtar da shi gami da mahaifansa Yasir da Sumayya abin da ya yi sanadiyyar shahadar mahaifan nasa, shi kuma Ammar ya kasa daurewa da irin wannan azaba har sai da ya yi maganganu marasa kyau ga Annabi sannan suka rabu da shi.
Da ya koma wurin manzon Allah tsirar Allah ta tabbabata gare shi da Iyalan gidansa yana kuka, da Manzo ya tambaye shi cewa, ya ya yake ji? Ammar ya tabbatar da cewa daram yake ji a zuciyarsa. Sai Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi da Iyalan gidansa ya ce,” Ammar yana cike da Imani tun daga kwakwalwar kansa har zuwa akaifar kafarsa, idan gobe suka kara yi maka irin wannan ka kara yi masu”. Wannan ya sa Allah (T) ya saukar da aya “ sai wanda aka tursasa shi, alhali zuciyarsa na cike da Imani”
Malam Yakubu ya kuma karanto Hadisai na Annabi a ruwayoyin Ahlulsunna da dama, da suka nuna ana yin Tukiyyah idan bukatar yin nata ta taso. sannan ya ce ya kamata a kara bincikawa domin a fahinci yadda al’amarin yake. Sannan ya ce, wannan batu na Tukiyya ya samo asali ne tun a farkon Musulunci, ba ‘yan Shi’a ba ne suka kirkiro, amma su suka fi yinta sabo da halin da suka sami kansu na takura da fafara da ake yi masu alokacin mulkin Umayyawa da Abbasiyawa, sai ya zamo sune suka fi bukatuwa zuwa ga yinta. Su kuwa Sunna basu shahara da yinta ba saboda basu da matsala da mahukunta, bilhasilima sune suke bayar da fatawa ga mahukuntan.” Wannan ya isa hujja ga mai neman gaskiya “
Malam Yakubu ya kara karanto wasu ruwayoyi da suka nuna yadda Sahabban Manzon Allah suka rika yin ta bayan rasuwar manzon Allah saboda abubuwan da suka biyo bayan rasuwar ta Annabin. Sai ya bayyana bukatar Musulmi su kara karantar Musuluncin domin kauce ma shiga cikin hadari.
Thursday, August 19, 2010
ISMA NA GUDANAR DA AIKIN TAIMAKO A BABBAR ASIBITIN GWAMNATIN JIHAR KATSINA
DAGA: ABDULKWANARYA
‘Yanuwa musulmi almajiran Malam Ibrahim Zakzaky(H) na sashen kiwon lafiya (ISMA) na Katsina, sun dauki aikin kulawa da majinyata a babbar Asibitin gwamnati da ke Katsina, sakamakon yajin aikin da ma’aikatan lafiyar jihar suka shiga a ‘yan kwanakin nan.
Malam Abdul Karim Usamatu wanda ke jagorantar wannan aiki ya bayyana haka ga manema labarai a Asibitin cewa, sun kawo wannan dauki ne, sakamakon wannan yajin aiki da ake yi a wannan jiha. Da yake bayyana irin aikin da suke yi a Asibitin, ya ce, suna duba marar sa lafiya ne idan suka gano abinda ke damunsa sai su bashi abinda suka tanada na magani, maganin da ba su da shi kuwa sai su sa aje a sayo, sannan suna bayar da maganin ne a kyauta. Ya tabbabatar da cewa, wannan aiki na al’umma ne” muna yi ne saboda ita al’ummar bata yi ba, amma shi wannan dauki na irin abinda muke yi , ya kamata ne ita al’ummar baki daya ta zo ta yi, domin wannan yajin aiki yana shafar mu ne duka” Sai ya yi kira ga sauran jama’a da su shigo a hada hannu a yi wannan aiki tare.”
Kodayake mun tarad da abokan aikinmu ‘yan Red Cross, ‘yan agaji na kungiyar Izala, Hizba, ‘Yan agaji na Jama’atu Nasril Islam da kungiyar dalibai da aka fi sani da (scout) suna ta kokari, saboda yanzu mun hada hannu ne tare da su muna gudanar da aikin” ya koka da rashin kayan aiki, amma duk da haka ya ce, suna gudanar da aikin.
Ya bayyana cewa bayan kulawa da marasa lafiya da suke yi, akwai kuma wani yunkuri da tuni suka fara na tsaftace Asibitin baki dayanta domin tsoron da suke da shi na barkewar cututuka saboda kazantar da yajin aikin ya haifar a Asibitin.
Ya yi bayanin yadda suka kasa aikin na su zuwa kashi uku , ta yadda wasu za su yi aikin safe wasu na rana wasu kuma na dare domin samun saukin gudanar da aikin .
Malam Abdul Karim Ya yi kira ga gwamnatin jihar ta Katsina da ta sasanta da ma’ikatan domin kulawa da lafiyar al’umma lallai gwamnati ce zata iya daukar nauyinsa. Ya jadda bukatar gwamnatin ta saurari wadannan ma’aikata tare da sasantawa da su domin mutane suna tagayyara sosai.
A karshe ya yi kira ga masu hali a fadin jihar da su kai dauki a wuraren da yajin aikin ya shafa domin samun sauki ga wadannan bayin Allah, tare da yin godiya ga Malam Zakzaky(H) wanda akan koyarwarsa ne har aka iya hada mutane masu masaniya a harkar lafiya daban –daban wuri daya suna gudanarda wannan agaji.
Wasu jama’a da da dama da da suka bayyana mana ra’ayinsu akan wannan yajin aiki, sun bayya muhimmancin sasantawa da ma’aikatan tare da bayyana takaicin ganin yadda gwamnati ta yi biris da al’amarin har aka shiga mako na biyu alhali majinyata suna cikin halin kaka ni kayi
Gabadayan Asibitin ta Katsina duk inda ka zagaya baka ji motsin jama’a sai dan abinda ba a rasa ba da suka yi saura, yayin da kasuwa ta bude ma Asibitin kudi ta gwamnatin tarayya da na masu zaman kansu saboda tururuwar da masu hali ke yi da majinyatansu, su kuwa marasa hali kodai sun koma gida ko sun hakura sun zauna a Asibitin jihar har zuwa wannan lokaci da Allah ya kawo wadannan masu bayar da agaji gare su.
‘Yanuwa musulmi almajiran Malam Ibrahim Zakzaky(H) na sashen kiwon lafiya (ISMA) na Katsina, sun dauki aikin kulawa da majinyata a babbar Asibitin gwamnati da ke Katsina, sakamakon yajin aikin da ma’aikatan lafiyar jihar suka shiga a ‘yan kwanakin nan.
Malam Abdul Karim Usamatu wanda ke jagorantar wannan aiki ya bayyana haka ga manema labarai a Asibitin cewa, sun kawo wannan dauki ne, sakamakon wannan yajin aiki da ake yi a wannan jiha. Da yake bayyana irin aikin da suke yi a Asibitin, ya ce, suna duba marar sa lafiya ne idan suka gano abinda ke damunsa sai su bashi abinda suka tanada na magani, maganin da ba su da shi kuwa sai su sa aje a sayo, sannan suna bayar da maganin ne a kyauta. Ya tabbabatar da cewa, wannan aiki na al’umma ne” muna yi ne saboda ita al’ummar bata yi ba, amma shi wannan dauki na irin abinda muke yi , ya kamata ne ita al’ummar baki daya ta zo ta yi, domin wannan yajin aiki yana shafar mu ne duka” Sai ya yi kira ga sauran jama’a da su shigo a hada hannu a yi wannan aiki tare.”
Kodayake mun tarad da abokan aikinmu ‘yan Red Cross, ‘yan agaji na kungiyar Izala, Hizba, ‘Yan agaji na Jama’atu Nasril Islam da kungiyar dalibai da aka fi sani da (scout) suna ta kokari, saboda yanzu mun hada hannu ne tare da su muna gudanar da aikin” ya koka da rashin kayan aiki, amma duk da haka ya ce, suna gudanar da aikin.
Ya bayyana cewa bayan kulawa da marasa lafiya da suke yi, akwai kuma wani yunkuri da tuni suka fara na tsaftace Asibitin baki dayanta domin tsoron da suke da shi na barkewar cututuka saboda kazantar da yajin aikin ya haifar a Asibitin.
Ya yi bayanin yadda suka kasa aikin na su zuwa kashi uku , ta yadda wasu za su yi aikin safe wasu na rana wasu kuma na dare domin samun saukin gudanar da aikin .
Malam Abdul Karim Ya yi kira ga gwamnatin jihar ta Katsina da ta sasanta da ma’ikatan domin kulawa da lafiyar al’umma lallai gwamnati ce zata iya daukar nauyinsa. Ya jadda bukatar gwamnatin ta saurari wadannan ma’aikata tare da sasantawa da su domin mutane suna tagayyara sosai.
A karshe ya yi kira ga masu hali a fadin jihar da su kai dauki a wuraren da yajin aikin ya shafa domin samun sauki ga wadannan bayin Allah, tare da yin godiya ga Malam Zakzaky(H) wanda akan koyarwarsa ne har aka iya hada mutane masu masaniya a harkar lafiya daban –daban wuri daya suna gudanarda wannan agaji.
Wasu jama’a da da dama da da suka bayyana mana ra’ayinsu akan wannan yajin aiki, sun bayya muhimmancin sasantawa da ma’aikatan tare da bayyana takaicin ganin yadda gwamnati ta yi biris da al’amarin har aka shiga mako na biyu alhali majinyata suna cikin halin kaka ni kayi
Gabadayan Asibitin ta Katsina duk inda ka zagaya baka ji motsin jama’a sai dan abinda ba a rasa ba da suka yi saura, yayin da kasuwa ta bude ma Asibitin kudi ta gwamnatin tarayya da na masu zaman kansu saboda tururuwar da masu hali ke yi da majinyatansu, su kuwa marasa hali kodai sun koma gida ko sun hakura sun zauna a Asibitin jihar har zuwa wannan lokaci da Allah ya kawo wadannan masu bayar da agaji gare su.
Friday, August 13, 2010
YADDA AKA FARA GABATAR DA TAFSIR NA BANA A KATSINA, MALAM YAKUBU YAHAYA KATSINA KE GABATARWA DUK SHEKARA A BABBAN MASALACIN JUMA'A NA KATSINA
DAGA ABDULKWANARYA, KATSINA.
A yammacin ranar Lahadi 28/08/1431. Aka fara gabatar da tafsirin Al'Qur'an mai tsarki na watan Ramadan na wannan shekarar ta 1431, da Da'irar 'yan uwa Musulmi Almajiran Malam Ibraheem Zakzaky (H) ke gabatarwa a karkashin jagorancin Malam Yakubu Yahaya Katsina a harabar babban Masalacin Juma'a na cikin garin Katsina.
A gabatarwar da ya yi, Malam Yakubu ya bayyana muhimmacin wannan watan na Ramadan da cewa wata ne da aka saukar da Al'qur'ani a cikin sa, sannan hadisai da dama sun yi bayani akan mahimmacin karatun Al'qu'ani a cikin watan, ya kara da cewa daga cikin mahimmancin kuwa har da tafsirin sa “ana karatun al'qu'ani ne domin fahimtar sa” ya kara da cewa mutum ya dauki Al'qur'ani ya yi ta karantawa. Wasu sukan yi kokari su sauke shi cikin kwana uku, wasu kwana shida gwargwadon zuruf din mutun”
Malam Yakubu ya karanto hudubar Manzon Allah da ya yi akan wannan wata na Ramadan, inda ya bayyana falalolin da Allah ya aje a wannan watan na Azumi, daga cikin wadannan falalolin har da cewa “barcin mai Azumi Ibada ne, addu'o'insa abin karbawa ne. Sai Manzo ya ce “ ku roki Allah ya baku damar azumtar wannan wata ya kuma baku damar karanta Littafin sa mai tsarki domin tababbe shine wanda aka haramta masa gafarar Allah a wannan wata.” Sannan Manzon Allah ya yi umarni da bayar da sadaka gami da ciyar da marasa galihu, ya kuma yi umarni da girmama manya da kuma tausaya ma yara. Sai Malam Yakubu ya nuna muhimmancin cewa ya kamata mutun ya dora ne da irin wadancan dabi'un ba kawai sai a lokacin watan Ramadan ba.
Sannan ya ce kamata ya yi mai Azumi ya kame daga kallace-kallace da sauran abubuwan da basu kamata a gani ba, domin mai Azumi ana bukatar kowace gaba tasa ta yi Azuminne ba kawai barin cin abinci ko na sha ba.
Daga cikin abubuwan da Manzo ya kwadaitar akwai kyautata dabi'u a wannan lokaci, ya karanto, cewa wanda duk dabi'unsa suka kyautata a wannan wata, ya sami shedar ketare siradi a ranar da diga-digai ke darjewa, sannan wanda ya tausaya ma wanda ke kasansa, Allah za ya saukake masa Hisabi. Sannan wanda ya yawaita yi ma Manzo da Iyalan gidansa Salati, Allah za ya nauyaya mizanin sa, wanda kuma ya karanta ayar Qur'ani kwara daya a wannan wata, daidai ya ke da wanda ya sauke Qur'ani a wani watan da ba Ramadan ba.
Wannan wata ne da ake bude kofofin Aljanna, ku roki Allah kada ya kulle ma kamu su, kuma wata ne da ake kulle kofofin wuta, ku roki Allah kada ya bude ma maku su.
A karshe Malam Yakubu ya tsoratar da cewa, “kadda ayi buda baki da haramun” sannan ya jawo hankalin jama'a da cewa kadda ya zama babu banbanci tsakain Azuminka da lokacin da ba azumi ka ke yi ba.
Shi dai wannan Tafsiri an saba gabatar da shi a irin wannan lokaci na Azumi tun tsawon shekaru ashirin da daya da suka gabata.
A yammacin ranar Lahadi 28/08/1431. Aka fara gabatar da tafsirin Al'Qur'an mai tsarki na watan Ramadan na wannan shekarar ta 1431, da Da'irar 'yan uwa Musulmi Almajiran Malam Ibraheem Zakzaky (H) ke gabatarwa a karkashin jagorancin Malam Yakubu Yahaya Katsina a harabar babban Masalacin Juma'a na cikin garin Katsina.
A gabatarwar da ya yi, Malam Yakubu ya bayyana muhimmacin wannan watan na Ramadan da cewa wata ne da aka saukar da Al'qur'ani a cikin sa, sannan hadisai da dama sun yi bayani akan mahimmacin karatun Al'qu'ani a cikin watan, ya kara da cewa daga cikin mahimmancin kuwa har da tafsirin sa “ana karatun al'qu'ani ne domin fahimtar sa” ya kara da cewa mutum ya dauki Al'qur'ani ya yi ta karantawa. Wasu sukan yi kokari su sauke shi cikin kwana uku, wasu kwana shida gwargwadon zuruf din mutun”
Malam Yakubu ya karanto hudubar Manzon Allah da ya yi akan wannan wata na Ramadan, inda ya bayyana falalolin da Allah ya aje a wannan watan na Azumi, daga cikin wadannan falalolin har da cewa “barcin mai Azumi Ibada ne, addu'o'insa abin karbawa ne. Sai Manzo ya ce “ ku roki Allah ya baku damar azumtar wannan wata ya kuma baku damar karanta Littafin sa mai tsarki domin tababbe shine wanda aka haramta masa gafarar Allah a wannan wata.” Sannan Manzon Allah ya yi umarni da bayar da sadaka gami da ciyar da marasa galihu, ya kuma yi umarni da girmama manya da kuma tausaya ma yara. Sai Malam Yakubu ya nuna muhimmancin cewa ya kamata mutun ya dora ne da irin wadancan dabi'un ba kawai sai a lokacin watan Ramadan ba.
Sannan ya ce kamata ya yi mai Azumi ya kame daga kallace-kallace da sauran abubuwan da basu kamata a gani ba, domin mai Azumi ana bukatar kowace gaba tasa ta yi Azuminne ba kawai barin cin abinci ko na sha ba.
Daga cikin abubuwan da Manzo ya kwadaitar akwai kyautata dabi'u a wannan lokaci, ya karanto, cewa wanda duk dabi'unsa suka kyautata a wannan wata, ya sami shedar ketare siradi a ranar da diga-digai ke darjewa, sannan wanda ya tausaya ma wanda ke kasansa, Allah za ya saukake masa Hisabi. Sannan wanda ya yawaita yi ma Manzo da Iyalan gidansa Salati, Allah za ya nauyaya mizanin sa, wanda kuma ya karanta ayar Qur'ani kwara daya a wannan wata, daidai ya ke da wanda ya sauke Qur'ani a wani watan da ba Ramadan ba.
Wannan wata ne da ake bude kofofin Aljanna, ku roki Allah kada ya kulle ma kamu su, kuma wata ne da ake kulle kofofin wuta, ku roki Allah kada ya bude ma maku su.
A karshe Malam Yakubu ya tsoratar da cewa, “kadda ayi buda baki da haramun” sannan ya jawo hankalin jama'a da cewa kadda ya zama babu banbanci tsakain Azuminka da lokacin da ba azumi ka ke yi ba.
Shi dai wannan Tafsiri an saba gabatar da shi a irin wannan lokaci na Azumi tun tsawon shekaru ashirin da daya da suka gabata.
Tuesday, August 10, 2010
Tuesday, August 3, 2010
BIKIN YAYE DALIBAN FUDIYYAH KATSINA KARO NA TAKWAS
Daga: Abdulkwanarya
An bayyana manufar samara da makarantun Fudiyyah da cewa, domin kawo gyara ne a cikin al’ummarrmu. Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Zakzaky(H) na Katsina ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen bukin yaye dalibai karo na takwas da makarantar Fudiyyah ta Katsina ta gabatar a dakin taro na Multi-Porpuse dake Filin Samji Katsina, a ranar 6/8/1431.
Malam Yakubu ya bayyana cewa, iyaye sun dauka tura yaro a makaranta ,yaro ya je ne mu huta da matala, bamu dauka muna gina wata al’ummaa ba ne. Sai ya yi kira da cewa,”babban abinda zaka ba yaro shine ilmi komai tsadar sa.
Da yake jawo hankalin iyayen su fahinci irin yanayin da wannan kasa take ciki na halin yanayin tabarbarewar al’umma, gami da lalacewar da kasar ta yi inda ta zamo sahun gaba a duniya wajen tabarbarewar al’amurra abinda da malamin ya bayyana da creewa ‘yan boko ne suka haifar da shi.Sai ya bukaci iyayen da su kara dagewa wajen daukar nauyin karatun yaran.”yaranmu sune jarin mu, sune za su kawo sauyin da ake nema”Sai ya yi fatan samun albarka ga wadannan yara.
A wani sashe na jawabin Malam Yakubu ya bayyana cewa, da yardar Allah a wannan shekara za a himmatu wajen samar da babbar kuma fadadaddar makaranta domin magance matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu. Ya kirayi ‘yanuwa gaba daya da su zamo cikin shiri domin tunkarar wannan aiki duk lokacin da aka bukata..
A tun da farko ,da yake gabatar da jawabi,Shugaban Makarntar MAlam Kabir Sani, ya bayyana irin nasarorin da makarantar take samu, wanda ya hada da samun nasarar cin jarabawar da makarantu a fadin jihar suke ta kokarin ganin dalibansu sun samu cinyewa, ya kara da cewa a duk lokacin wannan jarabawa ta Science Allah yana taimaka ma yaranmu su samun nasara inda yace "ko a bana ma yaranmu talatin da uku suika sami nasarar cin wannan jarabawa", ya kuma yi kira ga Da’irar Katsina ta himmatu wajen samar da makarantar sakandare wadda zata taimaka wajen kara tarbiyyantar da yaranmu akan lamarin wannan harka. ya nuna takaicin yadda yaranmu kan samu cikas da zaran sun fita daga fudiyyah sun koma wata makaranta.
An dai gabatar da kyaututtuka ga dalibnai masu barin makaranta da yahada da bayar da shedar kamala karatu “testimonial” gami da nada sabbin masu unguwanni da zasu kula wajen tafiyar da al’amurran dalibai.
An bayyana manufar samara da makarantun Fudiyyah da cewa, domin kawo gyara ne a cikin al’ummarrmu. Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Zakzaky(H) na Katsina ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen bukin yaye dalibai karo na takwas da makarantar Fudiyyah ta Katsina ta gabatar a dakin taro na Multi-Porpuse dake Filin Samji Katsina, a ranar 6/8/1431.
Malam Yakubu ya bayyana cewa, iyaye sun dauka tura yaro a makaranta ,yaro ya je ne mu huta da matala, bamu dauka muna gina wata al’ummaa ba ne. Sai ya yi kira da cewa,”babban abinda zaka ba yaro shine ilmi komai tsadar sa.
Da yake jawo hankalin iyayen su fahinci irin yanayin da wannan kasa take ciki na halin yanayin tabarbarewar al’umma, gami da lalacewar da kasar ta yi inda ta zamo sahun gaba a duniya wajen tabarbarewar al’amurra abinda da malamin ya bayyana da creewa ‘yan boko ne suka haifar da shi.Sai ya bukaci iyayen da su kara dagewa wajen daukar nauyin karatun yaran.”yaranmu sune jarin mu, sune za su kawo sauyin da ake nema”Sai ya yi fatan samun albarka ga wadannan yara.
A wani sashe na jawabin Malam Yakubu ya bayyana cewa, da yardar Allah a wannan shekara za a himmatu wajen samar da babbar kuma fadadaddar makaranta domin magance matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu. Ya kirayi ‘yanuwa gaba daya da su zamo cikin shiri domin tunkarar wannan aiki duk lokacin da aka bukata..
A tun da farko ,da yake gabatar da jawabi,Shugaban Makarntar MAlam Kabir Sani, ya bayyana irin nasarorin da makarantar take samu, wanda ya hada da samun nasarar cin jarabawar da makarantu a fadin jihar suke ta kokarin ganin dalibansu sun samu cinyewa, ya kara da cewa a duk lokacin wannan jarabawa ta Science Allah yana taimaka ma yaranmu su samun nasara inda yace "ko a bana ma yaranmu talatin da uku suika sami nasarar cin wannan jarabawa", ya kuma yi kira ga Da’irar Katsina ta himmatu wajen samar da makarantar sakandare wadda zata taimaka wajen kara tarbiyyantar da yaranmu akan lamarin wannan harka. ya nuna takaicin yadda yaranmu kan samu cikas da zaran sun fita daga fudiyyah sun koma wata makaranta.
An dai gabatar da kyaututtuka ga dalibnai masu barin makaranta da yahada da bayar da shedar kamala karatu “testimonial” gami da nada sabbin masu unguwanni da zasu kula wajen tafiyar da al’amurran dalibai.
Subscribe to:
Posts (Atom)