Sunday, July 15, 2012

AN GABATAR DA TARON YAUMUTTKLIF A DA'IRAR KATSINA


An bayyana takalifi da cewa shi ne a sa ka yin abinda  baka son yi, a  kuma  hana ka yin abinda kake  son ka yi. Malam Yakubu Yahaya  wakilin ‘yanuwa  almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) na da’irar  Katisna da kewaye  ne  ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi ga kananan yara  maza da matan  da suka kai shekarun  wajabcin shari’a  a kansu, a bukin “yaumut  taklif” wanda  dandalin matasa na yankin  ya shirya aka gabatar da  shi a ranar Lahadi  19/ 8/1433  a markazin ‘yanuwan dake  garin Katsina.

A farkon jawabin sai da Malam  Yakubu  ya kawo ma yaran wasu abubuwa da yara suka fi fifitawa, inda ya tambaye su abin da yaro ya fi bukata tsakanin ranaikun karatu  da kuma na hutun makaranta, ranar barci  da tashi ayi salla cikin lokaci  dangane  da sallar Asubahi  da dai  sauran misalai  makamantan wadannan. Sai ya  kara bayanin cewa, shi  takalifi baya  nufin Allah ya  dankara ma mutum aiki ne,  sai dai  domin a lahira Allah za ya canja ma mutum din ne da abin da ya hanu  a duniya  da   abinda  yake a lahira.
Malam Yakubu  ya  bayyana  ma yaran cewa, ana fara addini  ne  tun mutum  yana  yaro,  ba sai an girma ba ne ake  fara yinsa, sai  ya ce, idan ka ga tsohon  banza, to babu shakka yaron banza ya  taso, haka ma abin yake  idan  ka ga tsohon kirki, to ya taso ne a yaron kirki, inda ya ba yaran misalin  Shehu  Usman dan Fodiyo muijaddadi (RA)  yadda ya taso da kirki tun yana yaro ya kuma yi  rayuwar  kirki, ga kuma Imam Khomaini(KS) shi ma haka ya taso, kana Sayyid Zakzaky(H) shi ma  haka rayuwarsa  take, sai ya karfafa  cewa, duk inda ka ga yaron kirki  to za ya zama tsohon kirki, haka ma idan kaga sabanin wannan.  Sai ya tambayi  yaran ko akwai wanda ya ke so ya yi irin  tsufan  su Malam Zakzay (H), inda duk cikar su  suka amsa da cewa, E!. Sai ya yi fatan Allah (T)  ya tabbatar da haka.
 Malam  Yakubu, ya jawo hankulan  yaran da cewa, idan aka kai shekaru  irin nasu, to ba a bukatar  yaro ya bata Sallarsa  idan yana yi,  ko kuma ya boye ya ci wani abu idan yana Azumi,  ya ce , wanda duk ya yi haka ,to ana binsa  bashi sai ya rama su, idan ma azumi ne sai ya kara da guda  sittin(kaffara)  sakamakon bata daya da ya yi. Sannan ya kiraye su da cewa, ba a bukatar su zama masu karya , cin amana, su kuma zamo masu biyayya ga iyayensu, su kuima  lizimci yin amfani da  abubuwan  da  suke  koyo a makarantu na addini da aikatawa tun daga wannan rana har zuwa mutuwa. Sannan ya bukaci malamai da iyaye da su kara kulawa da sallar yaran a makarantu  da kuma gidajensu  har ya zamo sun saba. Sannan aka gabatar da salla raka’a  biyu wadda  Malam Yakubun  ya jagoranta  domin  koya ma yaran yadda ake bukatar su rika gabatar da ita a duk  sa’adda lokacin ta ya  gabato.
Shi dai wannan  biki na ‘yaumut taklifi’ an  gabatar da shi ne da zimmar  zaburantar da yaran da shekarunsu  suka  kama  daga tara zuwa sama  ga ‘yan mata, su kuma maza daga goma sha  biyar .
Saidai  a wanna karo an lura da cewa,  wadanda suka halarci wannan taro akwai kananan yaran da shekarun  nasu basu kai wadanda  aka bukata ba, abinda ya jawu yin kira da cewa, wasu sai an sake dawowa da su a wasu shekaru masu zuwa nan gaba, kamar yadda Malam Yakubu ya bukata.  An dai kammala wannan biki karo na  farko cikin nasara.


AN GUDANAR DA BIKIN YAYE DALIBAN FUDIYA TA KATSINA A KARO NA GOMA


A ranar Assabat 25/8/1433 da ya zo daidai 14/ 7 2012, makarantar Fudiyya Nursery and Primary Katsina ta gabatar da bikin yaye dalibanta karo na goma na wannan shekara wanda aka gabatar a unguwar Filin Sanji Katsina.

A jawabin da ya gabatar babban bako kuma Daraktan makarantar, Malam Yakubu Yahaya ya bayyana cewa, hakuri shi ne maganin dukkan matsala, ya tabo tarihin fara karatu a wannan makaranta inda ya bayyana yadda mkarantar ta somo tun ana karantarwa a zaurukan jama’a da aka ara, kama-kama har zuwa wannan wuri bayan samun damar ginawa, ya kara da cewa, duk da matsalolin da aka fuskanta, an sami nasarar kutsamasu ne saboda hakuri da malamai suka yi,amma bangare iyayen yara sun kasa yinirin  wannan hakuri da wadannan matsaloli saboda kasa tsayuwa da nauyin da ya rataya ga wuyansu ta fuskar sauke nauyin makaranta, daga nan Malam Yakubu ya bukaci iayaen da su samar da wani asusu wanda za su rika amfani da kudin suna juya su domin bayar da tallafi ga malamai dama  makarantar.

A yunkurin samar da makarantar sakandare da hadin gwiwar kwamitin ahl-duthour da Lajnar Fudiyya suka fara, Malam Yakubu ya yi tuni garesu da su yi kokari su samar da koda karamar Sakandare(JSS) ta yadda idan Dairar ta sami dama sai ta samara da babbar sakandare(SSS), sanna ya ce, idan zai yiwu yaran da za su fita shekara mai zuwa su  fara  da ita, musamman idan aka yi la’akari da  tabarbarewar tarbiyya a makarantu. Sannan Malam Yakubu ya bayyana cewa,”muna da babban guri akan yaranmu, tunda a yanzu komai ya ruguje a wannan kasa kuma babu wani abu da yake ginuwa a yanzu sai wannan harka”. Sai ya yi kira ga kungiyar tsofaffin dalibai na fudiyyar(FOSA) da su yi kokari su shige ma yaran makarantar  gaba domin  kawo ma makarantar ci gaba”.

A tun farko da yake gabatar da jawabi, shugaban makarantar Fudiyya, Malam Kabir Sani, godiya ya nuna ga da’irar “yanuwa ta Katsina akan fadada makarantar da ta yi, sannan ya bayyana shirin da ake yi na fara karatu bangaren Islamiyya  wanda za a fara gabatar da shi bayan dawowa hutun sabuwarv shekarar karatun makaranta.

An dai kammala wannan biki da bayar da kyaututtuka ga wasu iyaye da suka yi fice wajen bayar da gudunmuwa ga makaranta a wannan shekara tare da nada sabbin shugabannin dalibai na wannan shekara.  


Sunday, July 8, 2012

AN GABATAR DA BIKIN YAUMUT TAKLIF A GARIN KATISANA

An bayyana takalifi da cewa shi ne a sa ka yin abinda baka son yi, a kuma hana ka yin abinda kake son ka yi. Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) na da’irar Katisna da kewaye ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi ga kananan yara maza da matan da suka kai shekarun wajabcin shari’a a kansu, a bukin “yaumut taklif” wanda dandalin matasa na yankin ya shirya aka gabatar da shi a ranar Lahadi 19/ 8/1433 a markazin ‘yanuwan dake garin Katsina.
A farkon jawabin sai da Malam Yakubu ya kawo ma yaran wasu abubuwa da yara suka fi fifitawa, inda ya tambaye su abin da yaro ya fi bukata tsakanin ranaikun karatu da kuma na hutun makaranta, ranar barci da tashi ayi salla cikin lokaci dangane da sallar Asubahi da dai sauran misalai makamantan wadannan. Sai ya kara bayanin cewa, shi takalifi baya nufin Allah ya dankara ma mutum aiki ne, sai dai domin a lahira Allah za ya canja ma mutum din ne da abin da ya hanu a duniya da abinda yake a lahira.
Malam Yakubu ya bayyana ma yaran cewa, ana fara addini ne tun mutum yana yaro, ba sai an girma ba ne ake fara yinsa, sai ya ce, idan ka ga tsohon banza, to babu shakka yaron banza ya taso, haka ma abin yake idan ka ga tsohon kirki, to ya taso ne a yaron kirki, inda ya ba yaran misalin Shehu Usman dan Fodiyo muijaddadi (RA) yadda ya taso da kirki tun yana yaro ya kuma yi rayuwar kirki, ga kuma Imam Khomaini(KS) shi ma haka ya taso, kana Sayyid Zakzaky(H) shi ma haka rayuwarsa take, sai ya karfafa cewa, duk inda ka ga yaron kirki to za ya zama tsohon kirki, haka ma idan kaga sabanin wannan. Sai ya tambayi yaran ko akwai wanda ya ke so ya yi irin tsufan su Malam Zakzay (H), inda duk cikar su suka amsa da cewa, E!. Sai ya yi fatan Allah (T) ya tabbatar da haka.
Malam Yakubu, ya jawo hankulan yaran da cewa, idan aka kai shekaru irin nasu, to ba a bukatar yaro ya bata Sallarsa idan yana yi, ko kuma ya boye ya ci wani abu idan yana Azumi, ya ce , wanda duk ya yi haka ,to ana binsa bashi sai ya rama su, idan ma azumi ne sai ya kara da guda sittin(kaffara) sakamakon bata daya da ya yi. Sannan ya kiraye su da cewa, ba a bukatar su zama masu karya , cin amana, su kuma zamo masu biyayya ga iyayensu, su kuima lizimci yin amfani da abubuwan da suke koyo a makarantu na addini da aikatawa tun daga wannan rana har zuwa mutuwa. Sannan ya bukaci malamai da iyaye da su kara kulawa da sallar yaran a makarantu da kuma gidajensu har ya zamo sun saba. Sannan aka gabatar da salla raka’a biyu wadda Malam Yakubun ya jagoranta domin koya ma yaran yadda ake bukatar su rika gabatar da ita a duk sa’adda lokacin ta ya gabato.
Shi dai wannan biki na ‘yaumut taklifi’ an gabatar da shi ne da zimmar zaburantar da yaran da shekarunsu suka kama daga tara zuwa sama ga ‘yan mata, su kuma maza daga goma sha biyar .
Saidai a wanna karo an lura da cewa, wadanda suka halarci wannan taro akwai kananan yaran da shekarun nasu basu kai wadanda aka bukata ba, abinda ya jawu yin kira da cewa, wasu sai an sake dawowa da su a wasu shekaru masu zuwa nan gaba, kamar yadda Malam Yakubu ya bukata. An dai kammala wannan biki karo na farko cikin nasara.