Sunday, November 20, 2011

DA'IRAR YANUWA MUSULMI TA KATSINA TA GABATAR DA IDUL GADEER NA KWANA BIYU


Da irar ‘yanuwa musulmi almajiran Sayyid Zakzaky(H) ta  Katsina sun gabatar da taro na kwana biyu domin  murnar zagayowar ranar da Manzon Allah(S) ya ayyana magajinsa ga wannan al’umma watau Idil Gadeer  wanda wakilin ‘yanuwan na garin Malam Yakubu Yahaya ya gabatar a ranakun 20 da 21 ga watan Zulhijja  na wannan shekara ta 1432.

A zaman farko, Malam Yakubu ya karanto Hadisai ne masu dama daga cikin littafan magabata na Sunna  ba, da suke nuni da matsayi da fifikon Imam Ali (AS) akan sauran Saahabban Manzon Allah(S). Malam Yakubu ya ce, bamu ce sauran Sahabban Annabi basu da kima bane,sai dai abinda muka ce shine,daga Allah(T) sai Annabi A wajen daraja sannan sai Iyalan gidansa sannan Sahabbai suna bi masu a darja. Ya karanto HAdisan ne daga cikin littattafai irinsu Silsilatul-ahadisil maudu’ah ,al fada’ilu na Ahmad bn Hanbal, iqtibasu siradul mustaqima na ibni Taimiyyah da sauran Tafsirai da dama.Ya kara da cewa, ya kawo wadannan hujjoji ne domin tabbatar matsayi na Imam Ali(AS) domin masu musu su san cewa suna yin e da Manzon Allah(S), sannan ya kara da cewa, duk wadannan littattafai muna karanto sun e ba domin kkure basai domin mu gano gaskiya mu kuma yi riko da ita tunda matsaloli sun faru a wannan addini bayan wafatin Manzon Allah(S).

A rana ta biyu,Malam Yakubu ya karanto doguwar khudubar Manzon Allah wadda ya yi a wannan rana,ya karanto ta daga wasu littafai da suka kawo wani sashe na khudubar, sananan ya karanto ta a kammale daga ruwayar ahlul baiti(AS).
Ranar Gadeer, ran ace wadda Manzon Allah ya nada Imam Ali (AS) da umurnin Allah a matsayin Khalifarsa bayan wafatinsa.

A rana ta biyu bayan kammala wannan karatu, Malam Yakubu ya jagoranci  yanka cake na murnar wannan biki wanda ‘yanuwa na Acadamic forum suka tanada.An kamala wannan taro cikin nasara kamar yadda aka tsara tare da fatan Allah ya nuna mana zagayowar na badi.
















No comments:

Post a Comment