Sunday, November 20, 2011

DANDALIN MATASA YA GABATAR DA TARON MURNAR ZAGAYOWAR RANAR DA MANZON ALLHA YA NADA WAKILINSA


Dandalin matasa Na harkar musulunci a karkashin jagorancin Sayyid Ibarahim Zakzaky(H) dake garin Abukur dake karamar hukumar Rimi ta jihar Katsina sun gabatar da taron tunawa da Idul Gadeer a harabar makarantar Fudiyyah Islamiyya dake garin na Abukur a ranar Assabat 23/ 12/ 1432.


Malam Aminu Jakara wakilin ‘yanuwa almajiran Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) na Da’irar Rimi ne babban bako da ya gabatar da jawabi a wannan taro, ya bayyana wannan Idi na gadeer da cewa shine babban Idi kamar yadda aka tambayi Imam Ja’afarus Sadiq (AS) ko akwai wani Idi bayan idin karamar salla da babba da ake dasu , inda ya amsa da cewa, akwai wanda ya fisu, shine idil Gadeer watau ranar da Manzon Allah(S) ya ayyana Imam Ali (AS) wakilinsa bayansa.

Malam Aminu ya bayyana cewa, samun kanka a cikin wadanda suka yi wila’a ga Iayalan gidan Annabi ba dubararka ba ce, ni’ima ce daga Allah (T), domin wasu suna gaba ne da su, don  haka ya zama wajibi gode ma wanna ni’ima ta hanyar yin aiki.Ya ce kallon ayyukan  Sayyid Zakzaky (H) da kyakkyawar fahimta da aiki akan abinda Sayyid din ya ke kira akansa yana daga cikin godiya da wannan ni’ima.

Sai ya yi kira ga Matasan da su ribanci wannan lokaci na su na kuruciya kafin damar ta kubuce masu. Ya kara da cewa, zaka iya rasa dukiya  da makamancin haka  kuma ka riske ta, amma idan rayuwarka ta zo karshe baka ribance ta ba, to zaka yi nadamar ayyukan da baka yi ba, haka kuma matashi zai yi nadama idan bai yi abinda ya kamata ba har tsufa ya riske shi.Sai ya jawo hankalin matasan da su yi amfani da damar da suka samu ta fahimtar addini su yi aiki na tallafama addinin kafin damar ta kubuce masu musamman wannan lokaci da al’umma take yayin addini. Sannan ya yi kira ga matasan  da su rika tunanin  makoma Lahira domin kauce ma fadawa mummunar makoma a nan duniya da gobe kiyama. Ya shawarci matasan da cewa, kamata ya yi tunaninsu ya zama kaka  zasu taimaka ma al’umma ta fita daga wannan hali da take ciki na zalunci da rashin hukunci da littafin Allah. Sannan ya bukace su da s u kyautata dabi’unsu, su himmantu ga neman Ilimin addini da kauce ma tunanin tara abin duniya ko ta wane hali gami da sa tunanin tsamar da al’umma fita daga mawuyacin halinda   take a ciki na danniya. Sai ya yi fatan Allah ya kara taimaka ma matasan  wajen ganin sun tsayu akan yin abinda Sayyid (H) yake da fata akansa.

A tun farko sai da daya daga cikin jagororin dandalin matasan na Katsina, Shamsu ya gabatar da mai  jawabi inda ya bayyana makasudin wannan taro da cewa na taya juna murnar zagayowar ranar da Annabi (S) ne ya nada ma Al’umma  Imam Ali(AS)  matsayin jagora ne  a bayansa.

Kafin nan  sai da aka gabatar da wata tamsiliyya mai taken”da’awar  dandalin matasa” wadda ta yi nuni da rawar da y  kamata matasa su taka  wajen  janyo hankulan abokai akan su yi riko da addini tare da yin watrsi da duk wata dabi’ar da ta saba ma addinin.    






DA'IRAR YANUWA MUSULMI TA KATSINA TA GABATAR DA IDUL GADEER NA KWANA BIYU


Da irar ‘yanuwa musulmi almajiran Sayyid Zakzaky(H) ta  Katsina sun gabatar da taro na kwana biyu domin  murnar zagayowar ranar da Manzon Allah(S) ya ayyana magajinsa ga wannan al’umma watau Idil Gadeer  wanda wakilin ‘yanuwan na garin Malam Yakubu Yahaya ya gabatar a ranakun 20 da 21 ga watan Zulhijja  na wannan shekara ta 1432.

A zaman farko, Malam Yakubu ya karanto Hadisai ne masu dama daga cikin littafan magabata na Sunna  ba, da suke nuni da matsayi da fifikon Imam Ali (AS) akan sauran Saahabban Manzon Allah(S). Malam Yakubu ya ce, bamu ce sauran Sahabban Annabi basu da kima bane,sai dai abinda muka ce shine,daga Allah(T) sai Annabi A wajen daraja sannan sai Iyalan gidansa sannan Sahabbai suna bi masu a darja. Ya karanto HAdisan ne daga cikin littattafai irinsu Silsilatul-ahadisil maudu’ah ,al fada’ilu na Ahmad bn Hanbal, iqtibasu siradul mustaqima na ibni Taimiyyah da sauran Tafsirai da dama.Ya kara da cewa, ya kawo wadannan hujjoji ne domin tabbatar matsayi na Imam Ali(AS) domin masu musu su san cewa suna yin e da Manzon Allah(S), sannan ya kara da cewa, duk wadannan littattafai muna karanto sun e ba domin kkure basai domin mu gano gaskiya mu kuma yi riko da ita tunda matsaloli sun faru a wannan addini bayan wafatin Manzon Allah(S).

A rana ta biyu,Malam Yakubu ya karanto doguwar khudubar Manzon Allah wadda ya yi a wannan rana,ya karanto ta daga wasu littafai da suka kawo wani sashe na khudubar, sananan ya karanto ta a kammale daga ruwayar ahlul baiti(AS).
Ranar Gadeer, ran ace wadda Manzon Allah ya nada Imam Ali (AS) da umurnin Allah a matsayin Khalifarsa bayan wafatinsa.

A rana ta biyu bayan kammala wannan karatu, Malam Yakubu ya jagoranci  yanka cake na murnar wannan biki wanda ‘yanuwa na Acadamic forum suka tanada.An kamala wannan taro cikin nasara kamar yadda aka tsara tare da fatan Allah ya nuna mana zagayowar na badi.