A karo na biyar, Mu’assasatus Shuhada’u
a Harkar musulunci a Najeriya da Sayyid Ibrahim Zazaky(H) yake
yi ma jagoranci, ta shirya taron karama juna sani na ‘ya’yan Shahidan Harkar wanda yankin Shahid
Hamza da ke KAtsina ya shirya a garin
tun daga ranar Juma’a 29/5/ ha r zuwa 1/6/ 1433.
A jawaban da aka gabatar da suka kunshi muhadarori da masu
jawabai . Dokta Abdullahi Dan Ladi wanda
ya yi jawabi aklan ‘ Ilimi ginshikin rayuwa” ya
bayyana ilimin da cewa, haske ne da Allah yake jefa shi a
cikin zuciyar wanda ya ga dama, inda ya bayyana cewa, kowace halitta da Allah ya
samar, to tana da nata ilimi da aka kimsa mata sai dai ilimin yakan bambanta da na juna.
Dokta Abdullahi ya bayar da misalai akan
halittu na dabbobi da yadda suke rayuwa a tsakaninsu abisa ilimi da Allah ya hore masu, sai ya ce amma ilimi dan Adam ya bambanta dana dabba.
Dangane da ilimin Dan Adam, cewa ya
yi,akwai wanda mutum ya gada
kuma yake koyo acikin al’uimmar
da yake rayuwa a cikinta sannan wanda ake
koyowa a hannun malamai.
Dokta ya bayyana
cewa, rayuwar mutum bata takaita anan duniya ba, akwai wata rayuwar ta bayan
mutuwa, sai ya ce, duk wanda aka halitta , to za a yi masa Hisabi,
kuma ana yi ma mutum
Hisabinne gwargwadon Iliminsa , ya bayyana cewa, sai mutum ya san Mahaliccinsa sannan ne zaya iya bauta masa yadda ya kamata,
sannan dole aikin mutum ya tafi kafada da kafada da iliminsa. Sai ya bayyana
ilimin boko da cewa da shi da na addini duk daya ne matukar dai mutum ya
yi ilimin domin Allah da kuma niyyar taimakama al’umma. Ya kara da
cewa, kamar yadda za a iya yi ma mutum azaba akan ilimin boko, to haka ma za a
iya yin azabar ga mai ilimin addini madamar mai na addini bai
yi amfani da ilimin ba. Sai ya bayyana
al’amarin karatu da cewa, ba abune mai sauki ba sai an dage sannan ne ake
samunsa. Sai ya bukaci ‘ya’yan Shahidan da su dage su kokarta su taka duk wani fage na ilimi
da ake da shi, kuma a shirye Mu’assasar take
ta dauki nauyin duk dan Shahidin da ya
sami damar kara karatu kowane iri ne .
A jawabin da ya gabatar Malam Abdull Hamid Bello Shugaban wannan
Mu’assasa ta Shahidan Harkar musulunci, ya yi Magana ne akan kyawawan dabi’u,
inda ya karanto Hadisai masu dama da suke Magana akan matsayin dabvi’u masu
kyawu. Malam Abdul Hamid ya bayyana tarbiyya
da cewa, ita ce,yin aiki mai kyau da
barin maras kyau” Sannan ya bayyana cewa, Allah ya aiko mana da abin koyi watau
Manzon Allah (S) wanda yake rahama a cikin halittu,sannan wannan Manzo shine
madubi da zamu kalla domin koyon dabi’u daga wajen sa.Sai ya bukaci mahalarta da su
siffantu da duk dabi’u kyawawa na addini
kamar ,gaskiya ,hakuri, yakini akan abinda mutum yake yi ,kyauta da dabi’ar
mutunta kai”muru’a”ya kuma bukaci mahalarta su yi dubi cikin lamurransu domin siffantuwa
da irin wadannan dabi’u saboda da irinsu ne kawai za a iya kawo gyara a cikin
al’umma..
A jawabin kammal wannan taro da ya gabatar, Malam Yakubu Yahaya ya fara ne da gode ma Allah (T) da ya hukumta
yin wannan taro na ‘ya’yan Shahidai masu albarka a wannan Gari na Katsina,sai ya bayyana
Shahada da cewa, ita ce sirrin nasara ”bama addini ba har lamurran rayuwa ana bukatar sadaukarwa inada ya nusar ta hanyar kawo wasu misalan al’ummu da suka
sadaukar domin su kubutar da kansu daga
danniyar ‘yan mulkin mallaka inda ya
bayar da misalin gwagwarmayar mutanen Kenya da Aljeriya a yayin kwatar kansu daga Turawa,sannan ya ce.
Gwargwadon sadaukarwarmu, daidai nasara
da zamu samu sai ya nuna muhimmancin mu kara sadaukarwa akan wannan tafarki na Addini” yadda tarbiyya ta gurbata a wannan al’umma tamu, mafita
daga wannan yanayi yana bukatar sadaukarwa”. Malam Yakubu ya ce, Allah ya yi mana baiwar kasha 99 bisa dari domin ya albarkace mu da jagoranci
, kuma wannan jagoranci shi ne makami na nasar saura kashi daya ake bukatar mu aikata, wannan kashi guda kuma shi ne “ji da bi” ga wannan jagora . Malam Yakubun ya jawo
hankalin ‘ya’yan Shahidan da cewa, su tsayu akan abinda iyayensu suka sadaukar da rayuwarsun akansa
watau gwagwarmayar addini sannan su guji aikata duk abinda za ya bakanta ran
mahaifansu domin suna kawo masu ziyara lokaci-lokaci kamar yadda ya tabbata a
Hadisin Annabi(S) Ya kuma bukaci masu
kula da iyalan shahidan da s kara u kula
da abubuwan da yaran su kanyi , a kwabe su idan suka yi abin da
bai kamata ba. Ya tsoratar da yaran cewa, su guji yi kahon cewa, su ‘ya’yan
sahidai ne amma su basu yin aikin da iyayen nasu suka yi, inda ya ce
wannan ba zaya fitar da su ba a lahira sai dai idan sun yi aiki na kwarai . ya kuma ankarar akan al’amarin wayoyin yaran da
cewa, akwai bukatar a rika kulawa da
halin da wayoyin yaran suke ciki, domin akwai makircin bata tarbiyyar ‘ya’yanmu da aka bollo da shi ta
hanyar wayoyin tafi da gidanka.
A wannan mu’tamar an samu nasarar kai ziyarori a wuraren tarihi
da suka hada da Hasumiyar Gobarau,da Makabartar Dan Marna wani waliyyi da aka yi a Katsina sai zuwa rijiyar Gusugu dake birnin Daura tare da ziyatar
shahid Ibrahim Muhammad Zariya da ya sami shahadarsa a lokacin waki’ar janar Abacha.
Manufar shirya wannan taro dai kamar yadda
Malam Abdul Hamid ya bayyana ma almizan shi ne gina tarbiyyar ‘ya’yan shahidai
a tafarkin da iyayensu suka
sadaukar da rayukansu tare da wayar masu
da kawunansu akan muhimman wurare na tarihi dake cikin wannan kasa.