Daga: AbdulAzizi
MANUFAR BUDE WANNAN DANDALI NA MEDIAFORUM KATSINA, SHINE YADA HARKOKIN KIRAN DA MAULANA SAYYID IBRAHIM ZAKZAKY(H)YAKE YI NE.TARE DA KAWO LABARAN ABUBUWAN DA KE FARUWA NA WANNAN HARKAR TA MUSULUNCI A WANNAN YANKI NA KATSINA DAMA WASU YANKUNA, NA YUNKURIN WAYAR MA AL'UMMA KAI DANGANE DA AL'AMARIN MUSULUNCI, MUSAMMAN ABINDA YA SHAFI KOYARWAR AHLUL-BAITIN MANZON ALLAH(AS).
Saturday, February 18, 2012
YADDA AKA GABATAR DA TARON KARA MA JUNA SANI NA 'YANUWA 'YAN KASUWA A KATSINA
Kadan daga cikin hotunan da aka dauka yayin gabatar da taron karama juna sani na kwana biyu da 'yanuwa 'yankasuwa suka shirya a katsina, kwanakin baya.
Daga: AbdulAzizi
Daga: AbdulAzizi
Saturday, February 11, 2012
A CI GABA DA BUKUKUWAN MAULUDIN MANZON ALLAH, AN GABATAR DA FARETI A KATSINA
Akaro na biyu, Lajnar Islamiyyu ta harkar musulunci dake da’irar Katsina da kewaye, ta kaddamar da gasar farertin girmamawa ga Manzon Allah (S) na wannan shekara a ranar Assabat 19/3/1433, a Unguwar filin samji dake Katsina.
Makarantun islamiyyu, daga sassa daban-daban ne suka halarci wannan gasa, cikin makarantun da suka shiga wannan gasa, akwai Fudiyyoyin, Batagarawa,Magamar Jibiya,Rimi Abukur, Bindawa,sai Islamiyyu irinsu Baharul’Fatimiyya,Shabbabul’Mahadi,Tarbiyyatul’islam da sauransu,inda kowace makaranta ta fito ta gabatar da irin shirin da take da shi da zaya kayatar da faretin.
A jawabin da ya gabatar bayan Kammala wannan gasa, Malam Yakubu Yahaya Wakilin ‘yanuwa na Katsina, ya Godema daliban Makarantun ,malamansu tare da wadanda suka koyar da su irin wannan Fareti . Malam Yakubu ya bayyana cewa, irin duk abinda mutum zaya gabatar da zaya nuna murna ga samuwar Manzon Allah , to halal ne matukar ba ya sabama koyarwar Musulunci ba ne.Ya ce, ga masu ganin an zurfafa ga son Manzon Allah kuwa, “sai su nuna mana iyakar darajar Annasbi, mu kuma mutsaya a nan”.Daga nan sai ya kirayi iyaye da su kula sosai akan tarbiyyar ‘ya’yansu, musamman a wannan lokaci da makiya suke kirkiro da wasu hanyoyi na lalata tarbiyyar ‘ya’yan musulmi. Ga wadanda ‘ya’yansu suke da wayoyi kuwa ,ya kiraye su da su rika kulawa da irin abubuwan da suke cikin wayoyin yaran nasu don sanin halinda suke a ciki, sai ya ce mafita daga irin wannan tarko shine kusantar Allah (T) da ibadu tare da aza yaran bisa tsayuwa da ibadun,Ya yi nuni da cewa ,kada kaga yaranka yana karatu,wannan bai isa ba sai an kula da irin abokan da suke tare da su.
Ita dai wannan gasa ta fareti a tabakin Malam Yakubu Idris wanda shine shugaban Lajnar ta Islamiyyu, cewa ya yi, an shirya wannan gasa ce, domin girmamawa ga Manzon Allah(S) kuma wannan sababben abu ne cewa, idan wani wanda ake girmamawa ya kai ziyara a wasu kasashe, to ana shirya masa fareti, saboda haka wannan Lajna ta tsara gabatar da shi domin girmama Manzon Allah(S).
Makarantunn da suka samu nasara a wannan gasa ta bana, sune, Fudiyya Batagarawa a matsayin ta hudu, Baharul Fatimiyya ta uku, Fudiyyah Rimi ta biyu sai Tarbiyyatul Islam Marnar Kadabo matsayin wadda tazo zakara watau ta daya.
Ashekarar da ta gabata ne dai aka fara gabatar da irin wannan gasa a cikin tsare-tsaren bukukuwan Mauludi. An dai kamala gasar cikin nasara da farin ciki daga al’ummar da suka sami halarta.
Subscribe to:
Posts (Atom)