Saturday, January 21, 2012

DANDALIN MATASA NA YANKIN KANO YA ZIYARCI NA KATSINA


 
A ranar  Laraba ne  25/ n2/ 1433 A.H,tawagar ‘yanuwa na Dandalin matasa na yankin Kano, suka kawo ziyara ga takwarorinsu da ke  Katsina domin sada zumunci tare da gabatar da jawabai na karfafa juna.
A jawabin da ya gabatar , shugaban dandalin na matasan harkar musulunci a karkashin jagorancin Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) Malam Hafizu Dauda  Kano, ya ankarar da ‘yanuwa matasa na gwagwarmaya akan manufar wannan ziyara , inda yace,domi sada zumunci ne da tattauna yadda za a iya haduwa a  karfafa juna , sai  ya ce, akwai bukatar kowanensu ya kula da kansa ta hanyar  siffatuwa  da kyawawan dabi’u, ganin cewa a yanzu akwai gurbacewar  tarbiyya. Ya kuma ya karfafi  ‘yan  dandalin da suci gaba da nemo malaman harka, ko masana su  rika yi masu bayani akan wasu bangarori na harka, ya kuma yi kira ga Malaman harkar nan da kara sa kula su fahinci matsalolin matasan domin a shigowa  da magancce su.
A wani sashen jawabin , Malam Hafizu ya tunanatar da ‘yanuwan cewa,Sayyid (H)  ya bayyana matasa a maatsayin jari na wannan harka,sai ya nuna wajabcin siffantuwa da kyawawan ayyuka  kamar  yadda Sayyid din yake koyarwa, sannan ya  bukaci matasan su kauce ma munanan ayyuka da za su jawo suka ga wannan kira da Sayyid din ke ma jagoranci. ya kuma bukaci matasa su kara kulawa da al’amurran harka ta hanyar nazartar tarihinn kiran, yaddad  harkar ta taso da irin sadaukarwar da magabatanta suka yi  domin samun damar tsayuwa akan ta.Sai yayi kira akan dagewa da ibada ta hanyar azumomi da sallolin na da makamantansu. A karshen jawabin nasa, ya bukaci kowane matashi ya zamo yana da wata gudunmuwa da yake bayarwa a wannan harka domin ta ci gaba.
A nasa  jawabin, danuwa Sanusi  Idris Musa, jawo hankalin matasa ya yi ta hanyar nuna takaicin  yadda suke wahalar da maluman harka  ta yin watsi da shiryarwar da suke yi a kodayaushe, sai  ya bukaci matasan su sa tunani tare da nazartar maganganun  Maluman, da kuma yin aiki da su.Ya ce  koda  kashi Hamsin cikin Dari na maganganunsu  aka yi aiki da su, to  da an ga sauyi a rayuwar  matasan. Ya shawarci matasan da cewa, kowanensu ya  duba  ya ga inda yake da gajiyawa ya yi aiki domin gyara matsalarsa saboda ana yin wannan harka ne domin neman  yardar  Allah(T).
Malama Fatima Yusuf Ali , daya  daga cikin wadanda suka kawo ziyarar daga Kano, ta bukaci ‘yanuwa maza da mata da su himmatu akan neman sanin ilmomi tare da sanin ilimin computer da harkar internet  domin yada  da’awar  Malam (H),ta kuma  jawo hankali akan dagewa  dai  da mujahada  domin iya tunkarar halin da ake ciki a yanzu haka.

A jawabin godiya da ya gabatar, Shamsuddin  Ahmad  a madadin ‘yan dandalin na yankin  Katsina, ya nuna godiya  ga , maziyartan da wannan  ziyara da suka kawo masu , ya kuma yi fatan su ‘yan kwamitin za su yi amfani da duk abubuwan da suka ji a wannan zama.
An kammala wannan ziyara cikin nasara, kuma tuni bakin suka isa gida lafiya.