Sunday, October 16, 2011

ITTIHADUS SHU'ARA YANKIN KATSINA, KANO DA JIGAWA SUN GUDANAR DA TARON KARAMA JUNA SANI NA KWANAKI BIYU A KATSINA


Bangaren mawakan gwagarmayar musulunci karkashin jagorancin Sayyid Ibrahim Zakzaky(H) na yankin Kano , Katsina da Jigawa, sun shirya tare da gabatar da taron karawa juna sani (Mu’tamar) na kwana biyu da aka gabatar da shi a Markazin “yanuwa musulmi dake Katsina daga ranar Juma’a 17/11 1432 zuwa Lahadi 19/11/ 1432.



A jawabin da ya gabatar, a loacin kammala wannan Mu’tamar, Malam Yakubu Yahaya wakilin ‘yanuwa na Katsina, ya yi kira ga mawakan gwagwarmayan da su fahimci cewa, Allah (T) ya yi masu baiwa, don haka su yi amfani da ita wajen isar da sakon gwagwarmaya ta yadda za su wayar ma jama’a da kai akan bara’a da wilaya gami da fadakar da su zaluncin da ke tafiyar ra rayuwar al’umma musamman Musulmi, domin ita waka tana da wani tasiri a zukatan al’umma.Ya ce,amma akwai bukatar su mawakan su kasance masu kyawawan dabi’u a dukkan ma’amalarsu da sauran jama’a, gami da tsayuwa akan muahada, ta yadda za su iya ba harkar kariya, sannan akwai bukatar sakonsu ya rika fitowa daga zuciya, domin duk sakon da ya fito daga zuciya ,to dole ne ya ratsa zukata, amma wannan za ya samu ne kawai idan an dage akan mujahada , tsarkin niyya tare da yi domin Allah, sanna kuma abin da kake fada ya dace da abin da kake aikatawa.

A wani sashe na jawabin , Malam Yakubu ya bayyana wajabcin mawakan su dage wajen neman Iliomi na addini tare da sanin tarihin A’imma(AS) ta yadda za su iya bayyana hakikanin yadda suka suka rayu, domin wanda baya da sani akan abu babu yadda za ya iya yin bayani a kansa. Ya kuma yi kira ga mawakan da su himmatu wajen tsara wakoki a bangarorin Addini daban –daban da suka hada da Tauhidi ingatacce, Kyawawan dabi’u, Gudun duniya da sauran bangarori da dama kari akan na gwagwarmaya da na ahlu-baiti(AS). A karshe ya karfafa yin dukkan al’amari domin Allah.

Taron na kara ma una sanin na kwana biyu , ya sami halartar malamai da suka hada da ; Malam Shehu Karkarku, Malam Abdul Karim Usama, Malam Ibrahim Ya’u da Malam Abubakar Kofar Durbi, inda suka gabatar da jawabai a lokuta daban-daban, jawaban da suka hada da Muhimmancin Ilimi ga mawakin gwagwarmaya, makarimul akhlaq, gudunmuwar mawaka ga harkar Musulunci , kyautata dangantaka a tsakanin juna.

Mawaka daga yankin Kano da Katsina suka sami halartar wannan Mu’tamar da suka hada da Mustafa Limanci, Gambo dan kaka, Aminu Jakara Abdussalam Ibrahim da sauran mawaka da dama, tuni aka kammala taron a cikin nasara.
Wani sashe na mawakan da suka halarci taron

wasu daga cikin mahalarta suna sauraren jawabi